Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai
Published: December 28, 2025 at 4:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 28, 2025

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bar birnin Lagos a ranar Lahadi, 28 ga Disamba, domin ci gaba da hutun karshen shekara a Turai, kafin daga bisani ya wuce Abu Dhabi a Hadaddiyar Daular Larabawa.

An gayyaci Shugaba Tinubu ne don ya halarci taron Abu Dhabi Sustainability Week 2026, wanda ake shirin gudanarwa a farkon watan Janairu, inda manyan shugabanni daga bangaren gwamnati, ‘yan kasuwanci ke tattauna hanyoyin bunkasa ci gaba mai dorewa a duniya.

A cikin wata sanarwa da Mai bai wa Shugaban Nijeriya shawara na musamman kan yada labarai Mr. Bayo Onanuga, ya fitar, ta bayyana cewa Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, shugaban hadaddiyar Daular Larabawa, ne ya gayyaci Shugaba Tinubu domin halartar taron.

Sanarwar ta ce shugaban kasar zai dawo Nijeriya da zarar an kammala taron UAE din.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan
Next Post: Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea

Karin Labarai Masu Alaka

NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
  • Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.