Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025
Published: December 31, 2025 at 1:56 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya

Shekara ta 2025 na da muhimmanci ga Najeriya ta fuskar siyasa, tattalin arziki da tsaro don ita ce shekara ta 3 ta wa’adin mulkin shugaba Tinubu gabanin zaben 2027.

An wayi gari a watan Maris shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci a jihar Ribas da hakan ya dakatar da gwamna Siminalayi Fubara na tsawon wata 6 biyo bayan turka-turkar madafun ikon jam’iyya ko tasirin mulki tsakanin gwamnan da wanda ya gada tsohon gwamna ministan Abuja Nyesom Wike.

Duk da masu sharhi na ganin hakan na cike da muradun siyasa da biyewa Wike don rawar da ya taka ta kange dan takarar adawa Atiku Abubakar daga lashe zabe a 2023, shugaba Tinubu ya dage dokar kuma hakan ya dawo da Fubara karaga.

A dabarun siyasa Fubara ya sauya sheka ya dawo jam’iyyar APC ta shugaba Tinubu inda ya ba da hujja da nuna guguwar nan in ba da taimakon shugaba Tinubu ba da wani labarin a ke yi.

Bayan jita-jitar yunkurin juyin mulki da hukumomi ba su tabbatar da rundunar sojan Najeriya ta ba da bayanin tsare hafsoshi 16 da nuna sun aikata wasu laifuka ne da su ka sabawa aiki. Daga bisani shugaba Tinubu ya yi garambawul ga hafsoshin soja ya sauke su in ban da babban hafsan bayanan sirri. Har ila yau shugaba Tinubu ya nada tsohon babban hafsan rundunar soja Janar Christopher Musa a matsayin ministan tsaro bayan murabus din babban minista Muhammad Badaru. Masana tsaro irin su Dokta Yahuza Getso sun yi sharhi.

Duk da yunkurin Najeriya da sauran kasashen ECOWAS na dawo da kasashe uku da su ka fada mulkin soja, Nijar, Burkinafaso da Mali, ya ci tura har zuwa watan Yuli. Ministan wajen Najeriya Yusuf Tugga ya ce sun yi duk abun da ya dace don dawo da kasashen masu taken AES

Yayin da shugaba Tinubu ya nada Injiniya Saidu Muhammad ya maye gurbin shugaban hukumar raba fetur a cikin kasa Injiniya Farouk Ahmed wanda ya yi murabus bayan takaddama da attajiri Aliko Dangote bisa zargin amfani da kudi fiye da samunsa, majalisar dokoki kuma ta amincewa shugaban amfani da kasafin kudin bara da na bana har zuwa watan Maris na badi. Wannan dai shi ne karo na farko da hakan ke faruwa. Dan majalisar Abubakar Hassan Fulata ya yi bayanin kariya kan matakin da ‘yan majalisa su kea mince.

Hakanan shugaba Tinubu ya ba da umurnin janye jami’an ‘yan sanda daga tawagar rakiyar manyan mutane don tura su inda za su kula da asalin aikinsu na samarwa al’umma tsaro.

Ita kuma babbar jam’iyyar adawa ta PDP na kara rage tasiri don gwamnonin jam’iyyar na ficewa zuwa APC inda shugaban da jam’iyyar ta zaba a babban taron Badun Barista Tanimu Turaki ke fama da kalubale daga bangaren jam’iyyar na magoya bayan Wike.

Dambarwar iko da babban ofishin jam’iyyar, ya sa Turaki zargin gwamnatin APC da makarkashiya, in da ya bukaci shugaba Trump ya kawo dauki.

Jigon jam’iyyar tsohon gwamnan Jigawa Sule Lamido da ya kai jam’iyyar kara kotu don hana shi tsayawa takarar shugabanci, ya nuna alamun zai iya barin jam’iyyar don ya ce in ba ta gyara ba za ta iya rasa dukkan mukamai a zaben gaba.

Ba mamaki kai korafin Bishop Wilfred daga Binuwai zuwa majalisar dokokin Amurka kan zargin yi wa mabiya addinin kirista kisan kare dangi a Najeriya, ya ja wani harin Amurka a yankin jihar Sokoto da har yanzu ba cikekken bayanin yanda lamarin ya kasance, duk da gwamnatin Najeriya ta ce ta na da masaniya.

Cikin manyan juyayi a shekarar ta 2025 akwai rasuwar tsohon shugaba Buhari bayan kwanciya a asbiti a London, sai kuma Shehun malamin Sunnah Dokta Idris Abdul’aziz Dutesn Tanshi wanda ya rasu a gidansa a Bauchi bayan fama da jinya.

Allah ya yi wa babban Shehun malamin Islama na darikar Tijjaniya Sheikh Dahiru Usman Bauchi rasuwa, shi ma a Bauchi inda Sheikh Sharif Ibrahim Sale ya jagoranci yi ma sa sallar jana’iza.

Fatan alheri ga dukkan masu sauraro a yayin da mu ke marabtar sabuwar shekarar 2026.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/REVIEW-NIGERIA-2025-1.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka
Next Post: Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry

Karin Labarai Masu Alaka

Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Zata Mamaye Lebanon Labarai
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
  • Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.