Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya
Published: January 2, 2026 at 12:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Kasar Gambia ta ceto mutane 96, da gawarwakin wasu mutane bakwai, bayan jirgin ruwa dauke da fiye da bakin haure 200 ya kife a yammacin kasar, kamar yadda ma’aikatar tsaron Gambia ta fada a cikin wata sanarwa data bayar ranar Alhamis. Ma’aikatar ta kara da cewa ana ci gaba da aikin ceto.

Wannan shine mummunar hatsari na baya bayan nan akan hanya mafi hadari da bakin haure galibi daga Afirka ta yamma suke bi a kokarin da suke yi na isa Spain ko Andalusiya ta wani tsibiri da ake kira Canary Island.

An sami rahoton cewa jirgin ya kife ne a tsakiyar dare kusa da wani kauye daga bisani aka sami jirgin ya kafe cikin yashi a wani yanki na kasar dake arewaci, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta fada.

Kungiyar tarayyar turai tace bakin haure na ba safai ba dubu 46 ne suka isa tsibirin Canary a shekarar 2024, adadi mafi yawa da aka gani, fiye da mutane dubu 10 suka mutu a kokarin su na zuwa turai, wanda ya nuna karin kashi 58 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2023, inji wata kungiyar kare hakkin bil’adma da ake kira Caminando.

Amma alkaluma daga hukumar kula da shige da fice ta kunigyar tarayyar turai watau EU a takaice, tace a watanni 11 na shekarar 2025, an sami ragowar korarar irin wadanan mutanen daga Afirka ta yamma masu niyyar zuwa turai da kashi 60 cikin dari.

Hukumar shige da fice ta turai tace raguwar masu tafiya turan, ya ta’allaka ne kan matakan hana tafiye tafiye masu tsanani da kasashe da ake tashi cikinsu wadanda suke aiki da kungiyar tarayar turan suke dauka.

Akalla mutane 70 ne suka halaka cikin watan Agustan bara, lokacin da jirgin da suke ciki, da aka ce ya ta so daga Gambiya ya kife, a hatsari mafi muni da aka gani a cikin shekarun baya bayan nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai
Next Post: Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
  • Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.