Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Published: January 3, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Amurka ta hambare gwanatin shugaba Maduro a Venezuela, kuma tace zata gudanar da harkokin kasar har zuwa lokacin da ya dace. Shugaban Amurka Donald Trump ne ya bayyana haka a wani taron da manema labarai a Mar-Largo, wurin shakatawarsa dake jihar Florida.

Da manema labarai suka matsa neman karin bayani kan yadda Amurka zata tafiyar da harkokin kasar ta Venezuela, shugaba Trump bai bada amsa kai tsaye ba. Yace “zamu tafiyarda harkokin kasar da gungun mutane. Kuma zamu tabbatar da cewa an tafiyar da kasar yadda ya kamata.” inji shugaban na Amurka.

Da ‘yan jarida suka matsa don jin yadda za’a aiwatar da shirin, shugaba Trump, yace “ana yin haka a halin yanzu.” Muna zabar mutane. Muna magana da mutane. Kuma za mu sanar da ku ko su wanene wadan nan mutanne, inji shugaba Trump.

Da yake magana a taron na manema labarai, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, yace, Maduro ba shine halataccen shugaban Venezuela ba. Domin tun a shekara ta 2020 zamanin gwamnatin Trump ta farko Amurka ta tuhumi Maduro, haka itama gwamnatin Biden da kuma gwamnatiin Trump ta yanzu.

A taro da manema labaran, shugaba Trump ya gargadi shugaban kasar Columbia cewa ya shiga taitayinsa. Yana zarginsa da sarrafawa da safarar miyagun kwayoyi,  Da aka tambayeshi gameda kasar Cuba, shugaba Trump, yace akwai bukatar ita ma Cuba a dubi lamarinta domin tana bukatar taimako.

Da suke maida martani kan wannan mataki, wakkilan majalisar dokokin Amurka ‘yan jam’iyyar Democrat, sunce jami’an gwamnati Trump basu gaya musu gaskiya ba a ganawarda suka yi da su a baya bayan nan gameda Venezuela, suko jami’an bangaren zartaswa sun fada musu basu da burin sauya gwamnati a Venezuela.

 

Amurka, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a
Next Post: Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye Afrika
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.