Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona!
Published: January 4, 2026 at 1:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Jagoran Tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bukaci Gwamna Abba K. Yusuf da ya bar kujerar gwamna idan har yana shirin ficewa daga jam’iyyar NNPP.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wani taro da magoya bayansa da masu ruwa da tsaki a Kano, a daidai lokacin da ake rade-radin cewa gwamnan na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Ya ce ba daidai ba ne a kwace wa tafiyar Kwankwasiyya kujerar gwamna daya tilo da take da shi a fadin Najeriya.

“Idan APC tana da kusan gwamnoni 30, me ya sa sai gwamnan Kano? Shi ne kadai ya rage mana,” in ji Kwankwaso, yana mai cewa duk wanda ke tursasa gwamnan ya sauya sheka ya kamata ya gaya masa ya bar kujerar gwamna ya tafi.

Tsohon gwamnan ya bayyana halin da ake ciki a siyasar Kano a matsayin abin tayar da hankali, yana mai gargadin cewa rikicin ba zai amfani jihar ba.

Ya ce yana kokarin sasanta al’amura a bayan fage domin hana jihar fadawa matsala.

Kwankwaso ya jaddada cewa gwamnatin NNPP har yanzu tana da lokaci ta yi wa al’umma aiki, yana mai kira da a hada kai maimakon rikici, sannan kuma yayi Suka game da kiran komawa abin da ya kira “Gandujiyya”, yana mai cewa hakan ya nuna rarrabuwar siyasa a jihar.

Ya karyata ikirarin cewa NNPP ba ta da karfi a Kano, yana mai cewa jam’iyyar ce mafi rinjaye.

Jagoran Jam’iyar ya gargadi shugabancin APC da kada su raina Kano, yana mai cewa jihar na da muhimmanci kuma ya kamata a rika mu’amala da ita cikin taka-tsantsan.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC
Next Post: Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika
Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Magoya Bayan Manchester United Sun Bukaci A Siyar da Bruno Fernandes Bayan Rashin Nasara A Kan AC Milan Wasanni
  • Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
  • Hawan Sallah Daga Masarautar Kaltungo Nishadi
  • NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi Afrika
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
  • Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.