Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya
Published: January 11, 2026 at 10:06 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 11, 2026

CAF Ta fara Bincike Kan Rikicin Bayan tashi a Wasan Algeria Da Najeriya.

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta fara bincike a hukumance kan munanan abubuwan da suka biyo bayan wasan kwata-final na Kofin Kasashen Afirka tsakanin Algeria da Najeriya a daren Asabar,

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, CAF ta tabbatar da cewa ‘yan wasan Algeria da membobin ma’aikatan bangaren masu horaswa sun tunkari alkalin wasan jim kadan bayan an busa tashi a wasan.

An ruwaito cewa lamarin ya kara kamari yayin da wasu daga cikin ‘yan wasan Algeria suka bi alkalan wasa zuwa cikin hanyar tafiyarsa zuwa dakin hutawa da aka tanadar masa, wani abu da CAF ta kira “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya saba wa dokokin ladabtarwa na gasar.

CAF ta kuma bayyana cewa tana duba rahotannin rikicin da ya shafi ‘yan jarida da sauran ma’aikatan kafofin watsa labarai bayan tashi a wasan, yayin da tashin hankali ya bazu a wajen filin wasa.

Wasan Algeria da Najeriya, wanda aka buga a Marrakech, ya ƙare da 2-0 nasara ga Super Eagles, ta Najeriya sakamakon da ya haifar da yanayin hayaniya daga sansanin Algeria.

Hukumar ta tabbatar da cewa za a yi nazari sosai kan dukkan rahotannin wasanni, na gabatar da alkalan wasa, da kuma shaidun bidiyo a matsayin wani bangare na binciken.

CAF ta kara da cewa za a sanar da matakan ladabtarwa da suka dace da zarar an kammala binciken.

Wannan lamari na ci gaba da kara haifar da cece-kuce a wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Afirka, yayin da AFCON 2025 ke shirin shiga mataki mai muhimmanci na wasan dab da karshen.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa
Next Post: Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku

Karin Labarai Masu Alaka

Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers Wasanni
An Bude Gasar Bauchi Annual International Polo 2026 Wasanni
FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon Labarai
  • Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.