Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya
Published: January 11, 2026 at 10:06 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 11, 2026

CAF Ta fara Bincike Kan Rikicin Bayan tashi a Wasan Algeria Da Najeriya.

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta fara bincike a hukumance kan munanan abubuwan da suka biyo bayan wasan kwata-final na Kofin Kasashen Afirka tsakanin Algeria da Najeriya a daren Asabar,

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, CAF ta tabbatar da cewa ‘yan wasan Algeria da membobin ma’aikatan bangaren masu horaswa sun tunkari alkalin wasan jim kadan bayan an busa tashi a wasan.

An ruwaito cewa lamarin ya kara kamari yayin da wasu daga cikin ‘yan wasan Algeria suka bi alkalan wasa zuwa cikin hanyar tafiyarsa zuwa dakin hutawa da aka tanadar masa, wani abu da CAF ta kira “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya saba wa dokokin ladabtarwa na gasar.

CAF ta kuma bayyana cewa tana duba rahotannin rikicin da ya shafi ‘yan jarida da sauran ma’aikatan kafofin watsa labarai bayan tashi a wasan, yayin da tashin hankali ya bazu a wajen filin wasa.

Wasan Algeria da Najeriya, wanda aka buga a Marrakech, ya ƙare da 2-0 nasara ga Super Eagles, ta Najeriya sakamakon da ya haifar da yanayin hayaniya daga sansanin Algeria.

Hukumar ta tabbatar da cewa za a yi nazari sosai kan dukkan rahotannin wasanni, na gabatar da alkalan wasa, da kuma shaidun bidiyo a matsayin wani bangare na binciken.

CAF ta kara da cewa za a sanar da matakan ladabtarwa da suka dace da zarar an kammala binciken.

Wannan lamari na ci gaba da kara haifar da cece-kuce a wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Afirka, yayin da AFCON 2025 ke shirin shiga mataki mai muhimmanci na wasan dab da karshen.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa
Next Post: Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku

Karin Labarai Masu Alaka

FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
  • Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.