Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano
Published: January 14, 2026 at 8:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar wata matar aure mai suna Aishatu Umar, wadda ake zargin ta rasu sakamakon sakaci a aikin likitanci bayan an yi mata tiyata a asibitin Abubakar Imam.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Samira Suleiman, ta fitar a ranar Talata.

“Kwamitin Kula da Asibitocin jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Babban Sakatare, Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya lura da rahoton da ya tayar da hankula game da rasuwar Aishatu Umar.

“Muna miƙa ta’aziyyarmu ga iyalanta da masoyanta. Babban Sakatare ya bayar da umarnin a gaggauta gudanar da cikakken bincike kan zargin da aka yi a asibitin Abubakar Imam domin gano gaskiya da abin da ya faru,” in ji ta.

Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa binciken zai kasance a bayyane, ba tare da son zuciya ba, kuma cikin ƙwarewa, tare da ƙara da cewa za a ɗauki matakan da suka dace bisa ƙa’idoji idan aka tabbatar da wani sakaci.

Idan za iya tunawa cewa an rawaito marigayiya Aishatu Umar ta rasu ne bayan abin da iyalanta suka bayyana a matsayin zargin sakaci a aikin likitanci bayan an yi mata tiyata a asibitin.

A cewar wani ɗan uwanta, Mohammed, wanda ya wallafa a shafin Facebook, marigayiya Aishatu, matar aure mai ‘ya’ya biyar, ta rasu da misalin ƙarfe 1 na dare a ranar Talata bayan ta sha fama da ciwon ciki mai tsanani tun bayan tiyatar da aka yi mata a watan Satumba na 2025.

“Ta fara korafin ciwon ciki mai tsanani wanda ya ci gaba har tsawon watanni. Ta sha wannan ciwo na tsawon watanni huɗu,” in ji Mohammed.

Ya yi zargin cewa duk da yawan komawarta asibitin, ma’aikatan lafiya suna ba ta magungunan rage zafi ne kawai su sallame ta ba tare da yin cikakken bincike ba.

Mohammed ya ƙara da cewa sai kwanaki biyu kacal kafin rasuwarta ne aka yi mata cikakkun gwaje-gwaje da hotunan bincike (scanning), waɗanda suka nuna wai an bar almakashi guda biyu a cikin jikinta tun lokacin tiyatar watan Satumba.

“An fara shirye-shiryen yin gyaran tiyata, amma lokacin nata ya ƙare,” in ji shi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka
Next Post: Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Atiku: Zaben 2027 Zai Zamo Karo Na Karshe Da Zan Nemi Shugabancin Najeriya Afrika
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe Afrika
NEDC Ta Karyata Bada Tallafin Karatun MSc Da Ke Yawo A Kafafen Sadarwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF Wasanni
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Nwakali Na Dab Da Komawa Kungiyar PAC Omonia Ta Cyprus Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.