Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano
Published: January 14, 2026 at 8:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar wata matar aure mai suna Aishatu Umar, wadda ake zargin ta rasu sakamakon sakaci a aikin likitanci bayan an yi mata tiyata a asibitin Abubakar Imam.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Samira Suleiman, ta fitar a ranar Talata.

“Kwamitin Kula da Asibitocin jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Babban Sakatare, Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya lura da rahoton da ya tayar da hankula game da rasuwar Aishatu Umar.

“Muna miƙa ta’aziyyarmu ga iyalanta da masoyanta. Babban Sakatare ya bayar da umarnin a gaggauta gudanar da cikakken bincike kan zargin da aka yi a asibitin Abubakar Imam domin gano gaskiya da abin da ya faru,” in ji ta.

Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa binciken zai kasance a bayyane, ba tare da son zuciya ba, kuma cikin ƙwarewa, tare da ƙara da cewa za a ɗauki matakan da suka dace bisa ƙa’idoji idan aka tabbatar da wani sakaci.

Idan za iya tunawa cewa an rawaito marigayiya Aishatu Umar ta rasu ne bayan abin da iyalanta suka bayyana a matsayin zargin sakaci a aikin likitanci bayan an yi mata tiyata a asibitin.

A cewar wani ɗan uwanta, Mohammed, wanda ya wallafa a shafin Facebook, marigayiya Aishatu, matar aure mai ‘ya’ya biyar, ta rasu da misalin ƙarfe 1 na dare a ranar Talata bayan ta sha fama da ciwon ciki mai tsanani tun bayan tiyatar da aka yi mata a watan Satumba na 2025.

“Ta fara korafin ciwon ciki mai tsanani wanda ya ci gaba har tsawon watanni. Ta sha wannan ciwo na tsawon watanni huɗu,” in ji Mohammed.

Ya yi zargin cewa duk da yawan komawarta asibitin, ma’aikatan lafiya suna ba ta magungunan rage zafi ne kawai su sallame ta ba tare da yin cikakken bincike ba.

Mohammed ya ƙara da cewa sai kwanaki biyu kacal kafin rasuwarta ne aka yi mata cikakkun gwaje-gwaje da hotunan bincike (scanning), waɗanda suka nuna wai an bar almakashi guda biyu a cikin jikinta tun lokacin tiyatar watan Satumba.

“An fara shirye-shiryen yin gyaran tiyata, amma lokacin nata ya ƙare,” in ji shi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka
Next Post: Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu

Karin Labarai Masu Alaka

Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.