Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula
Published: January 15, 2026 at 3:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 15, 2026

Rundunar sojojin kasar Sham ta ce yau alhamis zata bude hanya domin fararen hula su fice daga wani yanki na lardin Aleppo da ake kara jibga sojoji cikinsa, a bayan kazamin fada da aka gwabza tsakanin dakarun na gwamnati da na Kurdawan cikin birnin Aleppo.

Wannan sanarwa da rundunar sojojin ta fitar cikin daren laraba, wadda ta ce fararen hula na iya ficewa ta hanyar da za a bude daga karfe 9 na safiya zuwa 5 na yamma agogon kasar, tana nuna alamun cewa ana shirin kai farmaki a garuruwan Dar Hafer da Maskana da yankunan dake kewaye da nan, masu tazarar kilomita 60 a gabas da birnin Aleppo.

Rundunar sojojin ta yi kira ga dakarun kungiyar SDF dake karkashin jagorancin Kurdawa da ta janye mayakanta zuwa tsallaken kogin al-Furat, wato zuwa gabas da inda ake takaddama a kai.

Tuni dai rundunar sojojin Sham ta tura karin dakaru zuwa yankin, a bayan da ta ce kungiyar SDF ma tana ta kara jibge sojojinta a wurin.

Gwamnati ta zargi kungiyar SDF da laifin kai hare-hare da jiragen drone na birnin Aleppo, ciki har da wani hari kan ginin gwamnatin lardin Aleppo jim kadan a bayan da wasu ministoci biyu suka yi hira da ‘yan jarida.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan
Next Post: Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland

Karin Labarai Masu Alaka

Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
  • Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
  • Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • ‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.