Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu
Published: January 16, 2026 at 12:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 16, 2026

Limamin addinin Islama daya ya sami shahara har ya sami lambobin yabo kan zaman lafiya a jahar Filato, Imam Abdullahi Abubakar ya rasu a Jos.

Marigayi Imam Abdullahi Abubakar ya shahara a duniya ne biyo bayan sadaukar da kai da yayi na bada kariya ga mabiya addinin Kirista fiye da dari uku, bayan ‘yan bindiga sun kai musu hari a kauyen Yalwan Gindin Akwati dake karamar hukumar Barkin Ladi a shekarun baya.

A ranar Alhamis goma sha biyar ga watan Janairun dubu biyu da ishirin ta shida, da misalin karfe tara na dare ne, Allah ya karbi ran Imam Abdullahi Abubakar bayan fama da rashin lafiya.

Malamin, wanda yayi limanci a karkara, musamman a yankin da a baya ake samun yawan tashin hankali, ya taimaka kwarai wajen wanzadda zaman lafiya da hadin kai tsakanin mabiya addinai da kabilu daban-daban, wanda ya kai ga har kasashen duniya irin su Amurka da Saudi Arebiya da kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatocin tarayya da na jahar Filato suka bashi lambobin yabo da adadinsu ya kai goma sha hudu.

A zantawarsa da wakiliyar GTA Hausa a Jos, Zainab Babaji, kafin rasuwarsa, Imam Abdullahi Abubakar ya bayyana cewa yana sauke hakkinsa na zama da kowa lafiya ne, kamar yadda Allah ya hori al’umma suyi, don haka ya sadaukar da ransa wajen ceton Kirista fiye da dari uku, a lokacin da ‘yan bindiga suka mamayesu.

Imam yace a dalilin ayyukan zaman lafiya da yayi, ya sami lambobin yabo, ya kuma je aikin Hajji banda ganawa da yayi da manyan shugabannin duniya ciki har da marigayi, shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari da wassu gwamnoni.

Malam Abdullahi Umar Hassan, na’ibin limamin masallacin da Imam Abdullahi Abubakar ya jagoranta, ya bayyana mamacin a matsayin mai son hada kan jama’a ba tare da nuna bambanci ba.

Malam Hassan yayi fatar Allah ya zabo wanda zai cike gurbin da Imam ya bari na wanzadda zaman lafiya.

Haka ma kafafen sada zumunta a yau Jumma’a sun cika da hotunan Imam Abdullahi Abubakar, musammman daga wadanda suka yi hulda dashi a lokacin da yake raye, suna bayyana alhininsu kan rashin dattijon, da zayyana irin ayyukan alkhairi da yayi na samadda zaman lafiya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260116-WA0025.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC
Next Post: Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
  • Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
  • An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.