Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka
Published: January 16, 2026 at 10:11 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dubbannan ‘yan kasar Cuba sun yi zanga-zanga a gaban ofishin jakadancin Amurka da ke Havana don nuna kin amincewa da mulkin kama karya da Amurka ke yi a yankunan su, biyo bayan kame shugaban Venezuela Niclas maduro.

Zaman doya da manjan da aka dade ana yi tsakanin Amurka da Cuba ya kara ta’azzara ne tun bayan da Amurkan ta kai farmaki Kasar Venezuela da yayi sanadiyar sojoji da jami’an leken asiri na Cuba 32, da ke bawa Maduro kariya, wannan ita ce karawa ta farko tsakanin sojin Amurka da na cuba cikin shekaru da dama.

Da yake jawabi ga masu zanga-zangar, yana me juya bayan sa ga ofishin jakadancin Amurka, shugaban kasar Cuba Miguel Diaz, sanye da Kayan soja, ya yi kira ga ‘yan kasar su ci gaba da hadin kai a yayin da ake fuskantar matsi daga Amurka.

Ya ce, masu mulkin mallaka, bama tsoron ku, kuma bama so ayi mana barazana, a yayin da ya juya yake nuna ofishin jakadancin da yatsa, ya kara da cewa ba zaku razana mu ba.

Ranar Lahadin da ta gabata ne, shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba wani man fetur ko kudi na Venezuela da zai kara shiga hannun Cuba, inda ya gargadi fadar gwamnatin Havana ta yi yarjejeniya kafin lokaci ya kure mata.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane
Next Post: Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.