Jama’a sun yi tururuwa suna dibar ganimar man dizel yayin da tankar mai ta faɗi a Legas
Tanka mai ɗauke da dizal ta kife a gadar Tincan Liverpool da ke yankin Apapa a jihar Legas, inda wasu mazauna unguwa da masu wucewa suka rika kwashe man da ya zube.
Lamarin ya faru da safiyar yau Litinin kuma Shaidun gani da ido sun ce jami’an kula da zirga-zirga ba su kai wurin nan take ba.
Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jihar Legas (LASTMA) ta ce an rufe gadar na ɗan lokaci, amma daga baya an sake buɗe ta bayan jami’an kashe gobara sun rage haɗarin man da ya zube.
Hukumar ta ƙara da cewa zirga-zirga ya inganta yayin da ake jiran motar ɗaukar tankar.
Hukumar ta kuma gargadi jama’a kan haɗarin irin wannan hali, tana tunatar da mummunan sakamakon da ya faru a baya a sassan ƙasar, inda mutane da dama suka rasa rayukansu yayin ƙoƙarin kwashe mai daga tankoki da suka kife.


