Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya
Published: January 20, 2026 at 4:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Bankuna a Najeriya sun bayar da rahoton karuwar rashin biyan bashi a daga magidanta da kamfanoni duk da cewa samuwar rance da bukatar sa sun karu, a cewar binciken yanayin bashi na babban bankin Najeriya (CBN) na zangon karshe na 2025.

Rahoton ya nuna cewa rashin biyan bashi ya karu a dukkan nau’ikan rance, ciki har da rancen dake da jingina da wanda bai da jingina, da kuma na kamfanoni.

Kananan gidaje da kamfanoni kanana sun fi fuskantar matsala saboda hauhawar farashi, tsadar makamashi, da karancin kudin shiga.

A bangaren manyan kamfanoni, rashin biyan bashi ya kai kashi 6% a wasu lokuta, yayin da sauran kamfanonin kudi suka samu matsakaicin rashin biyan bashi na kashi 6.2%, lamarin da ke nuna tsanani a bangarorin tsarin kudi.

Duk da haka, bankuna sun kara bayar da rance ga gidaje da kamfanoni, amma babban bankin Najeriya ya yi gargaɗin cewa karuwar rashin biyan bashi na iya lalata ingancin kadarori da rage karfin bankuna.

CBN ta kuma ba da shawarar inganta tsarin dawo da bashi da kiyaye ka’idojin banki don rage matsalar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas
Next Post: Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.