Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya kammala ziyara ta biyu ta shirye-shiryen aikin Hajjin bana.
Ziyarar ta gudana daga 4 zuwa 19 ga Janairu, 2026, inda aka mayar da hankali kan ƙarfafa tsare-tsaren aiki, da inganta haɗin gwiwa da hukumomin Saudiyya, tare da daidaita masu ba da hidima daga Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki domin su dace da ka’idoji da jadawalin Saudiyya.
A sanarwar da Ahmad Muazu, mataimaki na musamman ga shugaban NAHCON kan yaɗa labarai ya fitar a ranar Talata, yayin ziyarar, tawagar NAHCON ta gana da manyan hukumomi, da suka haɗa da Ma’aikatar Hajji da Umrah, Hukumar Jiragen Sama (GACA), Ma’aikatar Lafiya, da masu kula da Mashā’ir, masauki da abinci, jiragen sama, da ‘yan Najeriya mazauna Saudiyya, da tsarin huldar kafafen yaɗa labarai.
Daga cikin manyan nasarorin da aka cimma; akwai kulla yarjejeniyoyin hidima, ɗora kwangiloli da jadawalin jirage a dandalin Nusuk Masar, duba asibitoci a Makkah da Madinah, tabbatar da ƙa’idar gwajin lafiya, da daidaita tsarin na’urorin dijital da aiki.
NAHCON ta kuma yi taro da hukumar kula da alhazai ta jihohi da kamfanonin yawon buɗe ido, domin ƙarfafa aiki a kan lokaci, ƙa’idoji da ingancin hidima kafin Hajjin 2026.
Hukumar ta ce yanzu za ta shiga mataki na gaba na shiri, ciki har da kammala kwangiloli, ɗora bayanan maniyyata, da ci gaba da haɗin gwiwa domin tabbatar da Hajji mai sauƙi kuma cikin tsari.


