A ghana ba’a biya wasu manoman cocoa ba, lamari da ka iya jefa aikin kwasar amfanin gona mai zuwa cikin hadari, domin ‘yan kasuwar Cocoa daga ketare sun ki biyan manoman kai tsaye karkashn sabon tsari cinikayyar da Gwamnati ta fitar, wadda ya kawar da hakkin biyan manoma daga hukumar kula da harkokin Cocoa zuwa ‘yan kasuwar.
Bayan da aka sami damina mai albarka a bana, masu sayen Cocoa sun ki su bada ajiyar kudi kashi 60 cikin dari na amfanin gonar Cocoa da ake tsammani, matakin da yanzu ya jefa kasar ta biyu a noman cocoa a fadin duniya da kwantensa, kamar yadda majiyoyi uku wadanda suke da masaniya kan lamari suka fada, sai dai basu bada yawan amfanin gonar da yayi kwanten ba.
Hukumar kula da albarkatun Cocoa ta Ghana bata maida martani ba da aka nemi jin ta bakinta kan wannan batu.
A halinda ake ciki kuma, gwamnan babban banki a Afirka ta kudu Lesetja Kyanyago ya fada ranar talata cewa, akwai dukkan alamun cewa burin bankin na ganin tashin farashin kayayyaki bai haura kashi 3 cikin dari ba zai tabata.


