Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi
Published: January 22, 2026 at 11:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

Kwamitin Gudanarwar Hukumar Hajji ta Najeriya Ya Shigar da Ƙorafi ga Tinubu, Ya Nemi A Sauke Shugaban Hukumar Bisa Zargin Cin Hanci da Rashawa

Mambobin kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) sun rubuta wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu wasiƙa, suna neman a sauke shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Pakistan), bisa zargin cin hanci da rashawa, rashin ƙwarewa da cin zarafin mukami.

Wasiƙar, mai kwanan wata 19 ga Janairu, 2026, ta nuna cewa zarge-zargen sun haɗa da kashe kuɗaɗe ba tare da amincewar kwamitin ba, bayar da kwangiloli ba tare da bin dokokin BPP ba, da kuma karya ƙa’idojin tafiyar da harkokin kuɗi. Kwamitin ya kuma ce shugaban yana ƙarƙashin binciken EFCC.

Mambobin sun ce waɗannan matsaloli sun janyo raguwar amincewa da hukumar, tare da haifar da rashin jituwa da Masarautar Saudiyya, wanda hakan ya sa aka rage yawan maniyyatan Najeriya daga 95,000 a 2025 zuwa 50,000 a Hajjin 2026.

Kwamitin ya bayyana cewa ci gaba da barin Farfesa Usman a mukami na iya kawo cikas ga shirye-shiryen Hajji mai zuwa, tare da jefa Najeriya cikin haɗarin aiki da diflomasiyya.

Ƙoƙarin jin ta bakin sa ya ci tura, sai dai a baya ya ce koke-koken da ake yi a kansa suna da nasaba da hassada a cikin hukumar.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan
Next Post: Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.