Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya
Published: January 24, 2026 at 11:19 AM | By: Bala Hassan

Gwamnatin Tarayya Najeriya da Amurka sun amince su haɗa kai don inganta ’yancin addini da ƙarfafa tsaro a Nijeriya

Gwamnatocin Tarayya da ta Amurka sun cimma matsaya kan cewa daga yanzu za su haɗa gwiwa don inganta ’yancin yin addini tare da ƙarfafa tsaro a duk faɗin Nijeriya.

Yarjejeniyar ta biyo bayan taron farko na Guruf ɗin Aikin Haɗin Gwiwa na Amurka da Nijeriya wanda aka gudanar a Abuja a ranar Alhamis, 22 ga Janairu, 2026.

An kafa wannan Guruf ɗin Aiki ne sakamakon sanya Nijeriya a matsayin Ƙasa Mai Bada Matukar Damuwa (wato “Country of Particular Concern”) da Shugaban Amurka Donald J. Trump ya yi a ƙarƙashin Dokar ’Yancin Yin Addini ta Ƙasa da Ƙasa (International Religious Freedom Act).

Ta hanyar haɗin gwiwa ta ƙut-da-ƙut, manufofin Guruf ɗin Aikin su ne rage tashin hankali da ake yi wa ƙungiyoyi masu rauni a Nijeriya, musamman Kiristoci, da kuma samar da yanayi mai kyau da zai ba dukkan ’yan Nijeriya damar yin addinin su cikin ’yanci ba tare da cikas daga ’yan ta’adda, ’yan a-ware, ’yan fashi da makami, da ƙungiyoyin ’yan bindiga ba, ko kuma duk waɗanda ke son cutar da fararen hula ba tare da la’akari da addinin su ba.

A taron na Abuja, Mashawarci ga Shugaban Ƙasa kan Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribaɗu, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya wadda ta ƙunshi Ma’aikatun Gwamnati da hukumomi guda 10, yayin da Ƙaramar Sakataren Harkokin Waje ta Amurka, Allison Hooker, ta jagoranci tawagar Amurka wadda ta ƙunshi hukumomin tarayyar ƙasar guda takwas.

A takardar bayan taron wadda aka raba wa manema labarai a ranar Alhamis, an bayyana cewa tattaunawar dabaru a zaman da aka yi sun mayar da hankali ne kan fannoni da dama na batutuwa da ƙalubale inda haɗin gwiwar Amurka da Nijeriya zai inganta ’yancin yin addini tare da ƙarfafa tsaro a faɗin ƙasar nan.

Ɓangarorin biyu sun yi la’akari da cewa akwai fa daɗaɗɗiyar alaƙa a tsakanin ƙasashen biyu, wadda ta ginu bisa ƙimomin haɗin kai na al’ummomi masu bambancin ra’ayi, girmama doka da oda, da mutunta ikon ƙasa.

Ɓangaren Amurka sun yi maraba da bayanin sake daidaita albarkatun Nijeriya domin magance rashin tsaro, musamman a jihohin Arewa-ta-Tsakiya. Gwamnatocin biyu sun sake jaddada ƙudiri mai ƙarfi da ba ya sassauci na kare ƙa’idojin ’yancin yin addini, tare da buƙatar ɗaukar matakai na haɗin gwiwa, masu ɗorewa da aiki tuƙuru, domin haɓakawa da kare ’yancin faɗar albarkacin baki, taron lumana, da ’yancin addini ko aƙida ga kowa, daidai da Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya.

Mahartan taron sun kuma jaddada muhimmancin kare jama’a farar hula, musamman al’ummar Kirista masu rauni, da kuma ɗaukar matakin hukunta masu aikata tashin hankali.

Ɓangarorin biyu sun sake tabbatar da aniyar su ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci, ciki har da aiki tare ta fannin ayyukan haɗin gwiwa na aiki, samun damar amfani da fasaha, yaƙi da safarar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba, hana tallafa wa ta’addanci da kuɗi, da gina ƙarfin hukumomin tsaro da bincike.

Tawagar Amurka ta gode wa Nijeriya bisa matakan gaggawa da ta ɗauka na ƙarfafa tsaro ga al’ummar Kiristoci da ke cikin haɗari, da kuma ’yan Nijeriya na dukkan addinai da rayuwar su take fuskantar barazana sakamakon tashin hankali da ta’addanci.

An yanke shawarar cewa za a gudanar da taro na gaba na Guruf ɗin Aikin a Amurka, a wata ranar da ta dace da ɓangarorin biyu, wadda za a tsara ta hanyar hanyoyin diflomasiyya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali
Next Post: Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
“Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
  • Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
  • Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
  • Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.