Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC
Published: January 26, 2026 at 9:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayinda a yau Talata jami’iyyar APC a jihar Filato ke shirin karbar gwamnan jahar, Caleb Mutfwang, bayan ya chanza sheka daga jami’iyyar PDP, komitin shirye-shiryen karbar gwamnan yace matakin da gwamnan ya dauka domin hadin kan al’ummar jahar ne da samadda ci gaba.

A taron ganawa da manema labarai a Jos, fadar jaha Filato, shugaban komitin kuma tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai ta Najeriya, Ahmad Idris Wase yace chanza sheka da gwamnan jahar ta Filato yayi shine matakin farko na samun zaman lafiya da ci gaba a jahar da ta sha fama da rikita-rikita.

Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang ya sami gagarumin goyon bayan jama’ar jahar a karkashin jami’iyyar PDP, duk da jeka ka dawo da aka yi a kotuna daban-daban, bias cewa jami’iyyar PDP bata da tsari a matakin jaha, kafin zaben dubu biyu da ishirin da uku.

Honarabul Nuru Shehu shine tsohon mai ba gwamnan hajar Filato Caleb Mutfwang shawara a mazabar Jos ta Arewa, yace gwamnan bai nuna dattako ba.

Kafin komawar gwamnan na jahar Filato, Caleb Mutfwang zuwa jami’iyyar APC, an yi ta kai ruwa rana tsakanin ‘ya’yan jami’iyyar, wanda wadansu suka nuna basu kaunar shigansa jami’iyyar.

Alhaji Saleh Abdullahi Zazzaga na daga cikin wadanda suka tsaya kai da fata wajen ganin gwamnan ya tsallaka zuwa APCn yace irin ayyukan da gwamnan yayi shi yasa suka bukaci kasancewarsa a jami’iyya daya da shagaban kasa, ya kara da cewa sun riga sun bashi shugabancin jami’iyyar a jaha da ma tikitin shiga zaben gwamna a dubu biyu da ishirin da bakwai.

A zaben shekara ta dubu biyu da ishirin da uku dai gwamnan, Caleb Mutfwang ya yi fafata da shugaban jami’iyyar APC na yanzu, Farfesa Nentawe Yilwatda a takarar gwamna, wanda masu sharhi ke bada shawarar jira da kallon yadda siyasar jahar zata kasance nan gaba.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos a Najeriya

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260126-WA0031.mp3
Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka
Next Post: Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa Labarai
Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fiye Da Mutane 108 Sun Rasa Rayukansu A Ambaliyar Kenya Afrika
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
  • Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.