Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC
Published: January 26, 2026 at 9:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayinda a yau Talata jami’iyyar APC a jihar Filato ke shirin karbar gwamnan jahar, Caleb Mutfwang, bayan ya chanza sheka daga jami’iyyar PDP, komitin shirye-shiryen karbar gwamnan yace matakin da gwamnan ya dauka domin hadin kan al’ummar jahar ne da samadda ci gaba.

A taron ganawa da manema labarai a Jos, fadar jaha Filato, shugaban komitin kuma tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai ta Najeriya, Ahmad Idris Wase yace chanza sheka da gwamnan jahar ta Filato yayi shine matakin farko na samun zaman lafiya da ci gaba a jahar da ta sha fama da rikita-rikita.

Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang ya sami gagarumin goyon bayan jama’ar jahar a karkashin jami’iyyar PDP, duk da jeka ka dawo da aka yi a kotuna daban-daban, bias cewa jami’iyyar PDP bata da tsari a matakin jaha, kafin zaben dubu biyu da ishirin da uku.

Honarabul Nuru Shehu shine tsohon mai ba gwamnan hajar Filato Caleb Mutfwang shawara a mazabar Jos ta Arewa, yace gwamnan bai nuna dattako ba.

Kafin komawar gwamnan na jahar Filato, Caleb Mutfwang zuwa jami’iyyar APC, an yi ta kai ruwa rana tsakanin ‘ya’yan jami’iyyar, wanda wadansu suka nuna basu kaunar shigansa jami’iyyar.

Alhaji Saleh Abdullahi Zazzaga na daga cikin wadanda suka tsaya kai da fata wajen ganin gwamnan ya tsallaka zuwa APCn yace irin ayyukan da gwamnan yayi shi yasa suka bukaci kasancewarsa a jami’iyya daya da shagaban kasa, ya kara da cewa sun riga sun bashi shugabancin jami’iyyar a jaha da ma tikitin shiga zaben gwamna a dubu biyu da ishirin da bakwai.

A zaben shekara ta dubu biyu da ishirin da uku dai gwamnan, Caleb Mutfwang ya yi fafata da shugaban jami’iyyar APC na yanzu, Farfesa Nentawe Yilwatda a takarar gwamna, wanda masu sharhi ke bada shawarar jira da kallon yadda siyasar jahar zata kasance nan gaba.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos a Najeriya

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260126-WA0031.mp3
Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka
Next Post: Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya Siyasa
Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa Afrika
  • An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.