Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC
Published: January 26, 2026 at 9:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayinda a yau Talata jami’iyyar APC a jihar Filato ke shirin karbar gwamnan jahar, Caleb Mutfwang, bayan ya chanza sheka daga jami’iyyar PDP, komitin shirye-shiryen karbar gwamnan yace matakin da gwamnan ya dauka domin hadin kan al’ummar jahar ne da samadda ci gaba.

A taron ganawa da manema labarai a Jos, fadar jaha Filato, shugaban komitin kuma tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai ta Najeriya, Ahmad Idris Wase yace chanza sheka da gwamnan jahar ta Filato yayi shine matakin farko na samun zaman lafiya da ci gaba a jahar da ta sha fama da rikita-rikita.

Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang ya sami gagarumin goyon bayan jama’ar jahar a karkashin jami’iyyar PDP, duk da jeka ka dawo da aka yi a kotuna daban-daban, bias cewa jami’iyyar PDP bata da tsari a matakin jaha, kafin zaben dubu biyu da ishirin da uku.

Honarabul Nuru Shehu shine tsohon mai ba gwamnan hajar Filato Caleb Mutfwang shawara a mazabar Jos ta Arewa, yace gwamnan bai nuna dattako ba.

Kafin komawar gwamnan na jahar Filato, Caleb Mutfwang zuwa jami’iyyar APC, an yi ta kai ruwa rana tsakanin ‘ya’yan jami’iyyar, wanda wadansu suka nuna basu kaunar shigansa jami’iyyar.

Alhaji Saleh Abdullahi Zazzaga na daga cikin wadanda suka tsaya kai da fata wajen ganin gwamnan ya tsallaka zuwa APCn yace irin ayyukan da gwamnan yayi shi yasa suka bukaci kasancewarsa a jami’iyya daya da shagaban kasa, ya kara da cewa sun riga sun bashi shugabancin jami’iyyar a jaha da ma tikitin shiga zaben gwamna a dubu biyu da ishirin da bakwai.

A zaben shekara ta dubu biyu da ishirin da uku dai gwamnan, Caleb Mutfwang ya yi fafata da shugaban jami’iyyar APC na yanzu, Farfesa Nentawe Yilwatda a takarar gwamna, wanda masu sharhi ke bada shawarar jira da kallon yadda siyasar jahar zata kasance nan gaba.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos a Najeriya

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260126-WA0031.mp3
Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka
Next Post: Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
APC Ta Sauya Jerin ‘Yan Takararta Bayan Nazarin Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Fidda Gwani Afrika
Ga Fili Ga Doki Dambarwar APC Da ADC Najeriya
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • Gwamnan Gombe Ya Ƙara Tallafin N148.76bn Domin Aiwatar da Sabon Tsarin Albashi A Jami’ar Gombe Afrika
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.