Rundunar ƴansandan jihar Gombe ta tabbatar da mutuwar A’isha ƴar shekara 15 a yankin Kwami dake jahar ranar Talata.
A cewar Kakakin Rundunar ƴansandan, DSP Buhari Abdullahi, an aika yarinyar sayen waken suya ne a ranar Litinin, amma ba ta dawo gida ba.
Ya ƙara da cewa sai a ranar Talata ne a ga gawār yarinyar a wani faifan bidiyo a kusa da ƙauyukan Wakili da Tuguji na ƙaramar hukumar Kwami.


