Kasar Afirka ta kudu ta bukaci mataimakin jakadan Isra’ila da ya fice daga kasar cikin sa’o’i 72 ranar Jumu’a, inda ta zarge shi da laifin kassara alakar dake tsakanin kasashen biyu a sakonnin da yake wallafawa a kafafen sada zumunta yana batanci ga shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa, abinda ya sabawa ka’idar diplomasiyya.
Ma’aikatar harkokin kasashen waje ta kasar Afrika ta Kudu ta ce zata kori Ariel Seidman na ofishin jakadancin Isra’ila a kasar, kuma bata maraba da shi a kasar ta.
Seidman shi ne jakadan Isra’ila dake da mukami mafi girma a kasar Afirka ta Kudu tun bayan da Isra’ila ta dawo da jakadan ta gida daga kasar a shekarar 2023.
Awanni bayan nan itama Isra’ila ta mai da martani, ta wallafa a shafin ta na X cewa ta kori babban jakadan Afrika ta Kudu, Shaun Edward Byneveldt daga kasar ta, ta kuma umarci shi ya bar kasar cikin sa’o’i 72.


