Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya
Published: February 5, 2026 at 7:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan bindiga sun kashe mutane kimanin 100 a wasu hare-haren da suka kai kan wasu kauyuka biyu a yankunan tsakiya da kuma arewacin Najeriya, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da neman mutanen da suka kubuta da rayuka suke kuma farautar ‘yan bindigar.

A jihar Kwara dake yankin tsakiyar Najeriya, ‘yan bindiga sun kai farmaki a wani kauye mai suna Woro, inda suka kashe mutane masu yawa.

Gwamnan jihar ta Kwara, Abdulrazaq Abdulrahman, wanda ya ziyarci inda abin ya faru ranar laraba tare da wasu kwamandojin soja da sojoji kimanin dubu 1, ya fadawa wani dan jarida dake zaune a Amurka, Farooq Kperogi, cewar sun tabbatar da mutuwar mutane 75 ya zuwa lokacin da suka yi magana, amma kuma adadin yana iya karuwa yayin da ake ci gaba da neman mutanen da suka bace.

Tun da farko, wani dan majalisa mai wakiltar yankin ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane har 170 suka mutu.

Shi ma kwamandan birged ta 22 ta dakarun Najeriya dake Ilorin, Birgediya Janar Nicholas Rume, ya fadawa Malam Farooq Kperogi cewa sun shawo kan lamarin a yanzu.

Wannan shine hari mafi muni da aka gani cikin shekarar nan a wannan yanki mai iyaka da jihar Neja, inda ake fama da hare-haren ‘yan bindiga masu kai farmaki a kan kauyuka da satar jama’a don yin garkuwa da su tare da satar dabbobi.

Dan majalisar da yayi magana da kamfanin dillancin labaran Reuters ta waya, Saidu Baba Ahmed, yace ‘yan bindigar sun tattara mutanen garin, suka daddaure hannayensu ta baya, sannan suka kashe su. Haka kuma ‘yan bindigar sun cinna wuta a gidaje da shaguna.

A wani harin na daban kuma, ‘yan bindiga sun kashe mutane akalla 21 a jihar Katsina dake arewacin Najeriya, inda ‘yan sanda da mazauna garin suka ce wadannan mahara sun bi gida-gida suna harbe mutane.

Wannan harin ya kawo karshen sulhun da aka yi a tsakanin mutanen wannan gari da ‘yan bindigar watanni 6 da suka shige.

Wannan hari na jihar Katsina ya nuna irin halin kaka-ni-ka-yin da mutane suke ciki a yankunan karkara na arewacin Najeriya, wadanda suka nemi yin sulhu da ‘yan bindigar da suke addabar su.

Mazauna irin wadannan kauyuka a akasarin lokuta suna harhada kudade da abinci domin bawa wadannan ‘yan bindiga da nufin neman su kyale su.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai
Next Post: Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya Afrika
  • Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.