Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya
Published: February 5, 2026 at 7:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan bindiga sun kashe mutane kimanin 100 a wasu hare-haren da suka kai kan wasu kauyuka biyu a yankunan tsakiya da kuma arewacin Najeriya, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da neman mutanen da suka kubuta da rayuka suke kuma farautar ‘yan bindigar.

A jihar Kwara dake yankin tsakiyar Najeriya, ‘yan bindiga sun kai farmaki a wani kauye mai suna Woro, inda suka kashe mutane masu yawa.

Gwamnan jihar ta Kwara, Abdulrazaq Abdulrahman, wanda ya ziyarci inda abin ya faru ranar laraba tare da wasu kwamandojin soja da sojoji kimanin dubu 1, ya fadawa wani dan jarida dake zaune a Amurka, Farooq Kperogi, cewar sun tabbatar da mutuwar mutane 75 ya zuwa lokacin da suka yi magana, amma kuma adadin yana iya karuwa yayin da ake ci gaba da neman mutanen da suka bace.

Tun da farko, wani dan majalisa mai wakiltar yankin ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane har 170 suka mutu.

Shi ma kwamandan birged ta 22 ta dakarun Najeriya dake Ilorin, Birgediya Janar Nicholas Rume, ya fadawa Malam Farooq Kperogi cewa sun shawo kan lamarin a yanzu.

Wannan shine hari mafi muni da aka gani cikin shekarar nan a wannan yanki mai iyaka da jihar Neja, inda ake fama da hare-haren ‘yan bindiga masu kai farmaki a kan kauyuka da satar jama’a don yin garkuwa da su tare da satar dabbobi.

Dan majalisar da yayi magana da kamfanin dillancin labaran Reuters ta waya, Saidu Baba Ahmed, yace ‘yan bindigar sun tattara mutanen garin, suka daddaure hannayensu ta baya, sannan suka kashe su. Haka kuma ‘yan bindigar sun cinna wuta a gidaje da shaguna.

A wani harin na daban kuma, ‘yan bindiga sun kashe mutane akalla 21 a jihar Katsina dake arewacin Najeriya, inda ‘yan sanda da mazauna garin suka ce wadannan mahara sun bi gida-gida suna harbe mutane.

Wannan harin ya kawo karshen sulhun da aka yi a tsakanin mutanen wannan gari da ‘yan bindigar watanni 6 da suka shige.

Wannan hari na jihar Katsina ya nuna irin halin kaka-ni-ka-yin da mutane suke ciki a yankunan karkara na arewacin Najeriya, wadanda suka nemi yin sulhu da ‘yan bindigar da suke addabar su.

Mazauna irin wadannan kauyuka a akasarin lokuta suna harhada kudade da abinci domin bawa wadannan ‘yan bindiga da nufin neman su kyale su.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai
Next Post: Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja Afrika
Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
  • Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun Labarai
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.