Ministan sadarwan kasar Uganda, Chris Baryomunsi ya yi Allah wadai da samamen da sojoji suka kai gidan dan jam’iyyar adawa Bobi Wine a watan da ya wuce. Ya kuma shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa, Wine be aikata wani lefi ba, kuma yana da damar dawowa gidan sa.
Baryomunsi, wanda kuma shine mai magana da yawun gwamnati ya ce hukumomi zasu yi bincike kan lamarin.
Wine ya shafe makonni a boye, bayan da ya tsere daga gidan sa dake Kampala babban birnin kasar, awanni kafin sanar da shi ne ya zo na biyu a sakamakon zaben da aka gudanar ranar 15 ga watan Janairu, inda shugaba Yoweri Museveni ya yi nasarar lashewa.
Ranar 24 ga Watan Janairu ne, Wine ya ce sojoji sun afka gidan sa, har suka ji ma matar sa ciwo. Shugaban sojojin Uganda Muhoozi Kainerugaba, wanda da ne ga Yoweri Museveni ya musanta zargin cin zarafin matar Wine.


