Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
Published: February 11, 2026 at 9:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A lokacin da mazauna garin Doma dake jihar Katsinan Nigeria suka kulla yarjejeniyar sulhu da ‘yan ta’adda a watan Satumbar bara, kowa a kauyen yayi fatan hare-haren ‘yan ta’addar ya zo karshe, kuma manoma zasu samu suyi noma a gonakan su cikin kwanciyar hankali.

Da farko abin ya dore, amma ranar 3 ga wannan watan, ‘yan ta’addan dauke da bindigogi suka far ma kauyen, suna bi gida-gida suna harbe mutane, inda suka hallaka a kalla mutane 21, abinda ya wargaza yarjejeniyar da aka kulla a baya.

Wannan ya sa mutane a wasu kauyukan na Katsina, Kaduna, Sakkwato da Kuma Zamfara da suka kulla irin wannan yarjejeniya da ‘yan ta’adda suke zaman dar-dar na tsoron cewa ana iya kai musu farmaki a ko da yaushe.

A watan da ya wuce ne, ministan tsaron Nigeria Christopher Musa ya gargadi hukumomi a kauyukan da su guji kulla irin wannan yarjejeniya da ‘yan ta’adda, saboda hakan na kawo kalubale ga kokarin da hukumomin kasa ke yi na wanzar da tsaro, da kuma dokar kasa na hana yin tattaunawar sulhu da ‘yan ta’adda.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
Next Post: Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
“Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
  • Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.