A lokacin da mazauna garin Doma dake jihar Katsinan Nigeria suka kulla yarjejeniyar sulhu da ‘yan ta’adda a watan Satumbar bara, kowa a kauyen yayi fatan hare-haren ‘yan ta’addar ya zo karshe, kuma manoma zasu samu suyi noma a gonakan su cikin kwanciyar hankali.
Da farko abin ya dore, amma ranar 3 ga wannan watan, ‘yan ta’addan dauke da bindigogi suka far ma kauyen, suna bi gida-gida suna harbe mutane, inda suka hallaka a kalla mutane 21, abinda ya wargaza yarjejeniyar da aka kulla a baya.
Wannan ya sa mutane a wasu kauyukan na Katsina, Kaduna, Sakkwato da Kuma Zamfara da suka kulla irin wannan yarjejeniya da ‘yan ta’adda suke zaman dar-dar na tsoron cewa ana iya kai musu farmaki a ko da yaushe.
A watan da ya wuce ne, ministan tsaron Nigeria Christopher Musa ya gargadi hukumomi a kauyukan da su guji kulla irin wannan yarjejeniya da ‘yan ta’adda, saboda hakan na kawo kalubale ga kokarin da hukumomin kasa ke yi na wanzar da tsaro, da kuma dokar kasa na hana yin tattaunawar sulhu da ‘yan ta’adda.


