A ranar Talata ne Majalisar ministocin kasar Zimbabwe ta amince da kudurin da zai sauya dokar kasa don bawa shugaban kasar Emmerson Mnangagwa damar kara wa’adin mulkin sa har zuwa shekarar 2030.
Wasu sauye-sauyen dokokin kasa da aka gabatar a gaban majalisar ministocin sun hada da bukatar ‘yan majalisa su rika zabar shugaban kasa, maimakon a bawa mutanen kasa damar kada kuri’a.
Ministan shari’a Ziyambi Ziyambi ya shaidawa taron manema labarai cewa za’a aikewa kakakin majalisa sabuwar dokar, kuma za’a wallafa ta a jaridar gwamnati kafin ‘yan majalisa su yi nazari a kan ta.
Wa’adin mulkin Mnangagwa, me shekaru 83 a duniya zai kare a shekarar 2028.


