Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya bayar da umarnin a fara biyan ma’aikatan jihar albashin watan Fabarairu nan take, domin sauƙaƙa musu shirye-shiryen tunkarar watan azumin Ramadan da ke ƙaratowa.
Sanarwar hakan ta fito ne a ranar Alhamis ta hannun shugaban sashen yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na ofishin gwamnan, Abubakar Bawa, inda ya bayyana cewa matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na tallafa wa ma’aikata da masu karɓar fansho a wannan lokaci mai muhimmanci ga al’ummar Musulmi.
A cewar sanarwar, matakin ya shafi ma’aikatan gwamnatin jiha, da na ƙananan hukumomi, da ma’aikatan Hukumar Ilimi ta Ƙananan Hukumomi, tare da tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho a faɗin jihar.
Sanarwar ta ƙara da cewa za a fara aiwatar da biyan albashin ne daga ranar Juma’a, 13 ga watan Fabarairu.
Ana sa ran al’ummar Musulmi a sassa daban-daban na duniya za su fara azumin watan Ramadan a ranar 18 ko 19 ga watan Fabarairu, gwargwadon yadda aka ga watan.
Matakin na gwamnan ya samu karɓuwa daga wasu sassa na al’umma, inda ake ganin hakan zai taimaka wa ma’aikata da masu fansho wajen gudanar da hidimomin rayuwa cikin sauƙi yayin azumi.


