Rundunar sojin Amurka na shirin shafe makonni suna kai hare-hare a Iran idan shugaba Trump ya bada umurnin da a kai mata farmaki, a cewar wasu jami’an Amurkan biyu da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters, abin da zai iya zama rigima mai tsanani fiye da wadda aka gani a baya tsakanin kasashen biyu.

Wannan abu da jami’an wadanda suka nemi a sakaya sunayen su saboda yanayin lamarin na takatsantsan da suka bayyana ya kara kaimin diplomasiyya kan tattaunawar da ake yi tsakanin Amurka da Iran
A makon da ya gabata ne Amurka da Iran suka zauna tattaunawa a Oman a yunkurin farfado da alakar diplomasiyya kan makaman nukiliya na Iran, bayan da Trump ya girke sojoji a yankin, abinda ya jawo fargabar barkewar yaki. A Jiya juma’a kuma Trump din ya ce zai kara aikewa da jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki a karo na biyu zuwa yankin gabas ta tsakiyan.


