Kimanin sojojin Amurka 100 ne suka isa Najeriya, yayinda hukumomi a Washington suke karfafa matakan yaki da ‘yan bindiga masu ra’ayin jihadi, kamar yadda kakakin sojojin Najeriya ya fada.
Amurka ta kaddamar da hare hare kan ‘yan tawayen da suke ikirarin musulunci cikin watan Disamba, yanzu kuma wata ‘yar tawagar sojojin Amurka suna aiki cikin kasar domin su taimakawa sojojin Najeriya wajen tattara bayanan sirri.
A cikin ‘yan kwanakin nan jiragen sama masu yawa dauke da sojojin Amurka da kayan aiki suna isa jihohin dake arewacin kasar, kamar yadda bayanai daga wani dandali dake sa ido kan zirga zirgan jiragen sama ya nuna, da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.
Kamar yadda kakakin helkwatar tsaro ta Najeriya, Manjo Janar Sama’ila Uba ya fada, dakarun na Amurka za su horasda sojin Najeriya tare da ba su shawarwari, amma ba za su je fagen daga ba.
Tun a farkon watan nan, rundunar sojin Najeriya tace ta na saran kimanin sojojin Amurka 200 za su isa kasar.
Ahalinda ake ciki kuma, ofishin kididdiga ta Najeriya ta fada jiya litinin cewa hauhawar farashin kayayyaki ya ragu a watan Disemban bara, daga 15.15 yanzu ya sauko zuwa kashi 15.10, wanda ya nuna saukar ko raguwar tsadar kayayyaki watanni 10 a jere.


