Ranar Litinin ministan harkokin wajen Iran ya gana da shugaban hukumar kayyade makaman Nukiliya na MDD, gabanin zaman shawarwari tsakanin hukumomi dake Washington da kuma Tehran, da zimmar warware takaddamakan shirin Nukiliyar Iran, da alamun babu bangare da yake nuna sassauci, yayinda Amurka take barazanar daukar matakin Soja kan Farisa.
Amurka wacce tare da Isra’la suka kai hare hare na hadin guiwa kan Iran a cikin watan Yunin bara, ta tura wani babban jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki na sama, wanda shine na biyu zuwa gabas ta tsakiya baya ga wasu jiragen ruwan yaki da tuni suke can, a yayinda ake zaman kallon hadarin-kaji tsakanin kasashen biyu.
Wani lamari da ya kara zaman dar dar shine ganin Iran ta fara rawar daji a mashigan ruwan Hormuz, wata muhimmiyar mashigar ruwa na kasa da kasa mai muhimmancin gaske ga kasashen larabawa da suke yankin Gulf, wadanda suka nemi a bi hanyoyin difilomasiyya wajen warware takaddamar.
A farkon watan nan ne Amurka da Iran suka sake farfado da shawarwari tsakanin su da nufin warware rikici kan shirin Nukiliyar Iran, wadda Washington da kawayenta a turai suke zargin na kera makamai ne, yayinda Iran kuma ta dage shirin ta na farar hula ne.


