Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika

Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi
Published: February 17, 2026 at 12:25 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gabanin shigowar watan azumin Ramadan, Church of Christ Evangelical and Life Intervention Ministry da ke Sabon Tasha a Kaduna ta raba kayan abinci ga Musulmi sama da 1,000, makarantun Islamiyya na Tsangaya da kuma wasu ‘yan gudun hijira (IDPs), a wani mataki da ke ƙara ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

An gudanar da rabon kayan ne a harabar Kano Road Central Mosque, inda Babban Faston Majami’ar, Dr. Yohanna Buru, ya bayyana cewa manufar shirin ita ce bunƙasa haɗin kai, juriya da zaman lafiya a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

A cewarsa, tsawon shekaru 20 da suka gabata, Majami’ar na tallafa wa Musulmi marasa galihu da makarantun Tsangaya a jihohin Arewa biyar da kayan abinci a duk lokacin Ramadan, domin ba su damar gudanar da azumi da ibada cikin walwala.

Ya ce ana raba shinkafa, masara da sauran kayan masarufi, tare da tabarmi da butocin roba, tare da ƙarfafa wa waɗanda suka amfana da tallafin gwiwar yin addu’o’in zaman lafiya da kwanciyar hankali ga ƙasa.

Fasto Buru ya kuma bayyana cewa, sakamakon tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki, ya tattara fastoci da limamai 50 domin gudanar da gangamin kwanaki bakwai tare da ‘yan kasuwa a kasuwanni, da nufin rage farashin kayan abinci domin sauƙaƙa wa al’umma a lokacin Ramadan.

Ya ƙara da cewa kowace shekara Majami’ar na taimakawa wajen biyan belin wasu fursunonin Musulmi, domin su samu damar yin azumi tare da iyalansu.

Haka kuma ya yaba da gudummawar da wata baiwar Allah Musulma, Hajiya Ramatu Tijjani, ke bayarwa duk shekara ga zawarawa da marayu a lokutan bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.

Babban Faston ya yi wa Musulmi a faɗin duniya fatan samun Ramadan mai albarka, tare da kira gare su da su ci gaba da yin addu’o’i domin dorewar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa.

Da yake karɓar kayan a madadin masu buƙata ta musamman, Shugaban Ƙungiyar Masu bukata ta musamman a jihar Kaduna, Malam Hassan Lawal, ya bayyana matuƙar godiya bisa wannan tallafi, yana mai kira ga attajiran Musulmi da su ƙara zage damtse wajen tallafa wa marasa galihu da kayan abinci domin su samu damar mayar da hankali ga ibada.

Haka zalika, Shugaban Ƙungiyar Makafi ta Jihar Kaduna, Malam Tukur Zubairu, ya yaba da yadda ake tunawa da su tsawon shekaru 20 a kowane watan Ramadan, yana mai cewa Allah ne kaɗai zai saka wa Faston bisa wannan karamci da kulawa.

A nasa jawabin, Imam Ibrahim Musa, wanda ya yi magana a madadin makarantun Tsangaya a Kaduna, ya gode wa Fasto Yohanna Buru bisa wannan tallafi, tare da kira ga sauran masu hali da su yi koyi da wannan kyakkyawan misali na zaman tare cikin lumana.

Shi ma Murshidin Jama’atu Nasril Islam, Imam Ilyasu, ya bayyana wannan mataki a matsayin gagarumin abin a yaba, yana mai kira ga masu hannu da shuni da su riƙa fitar da zakka da sauran sadaka domin tallafawa Musulmi marasa galihu, musamman a wannan lokaci na azumin Ramadan.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba
Next Post: Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma

Karin Labarai Masu Alaka

Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi
  • Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi
  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba Labarai
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.