An Fara Azumin Watan Ramadana Na Bana a Najeriya Da Sassan Duniya
A Larabar nan 18 ga watan Febrairu 2026 a ka fara azumin watan Ramadana a Najeriya, Saudiyya da kasashen musulmi da dama.
Wannan ya biyo bayan ganin jinjirin watan Ramadana yayin da watan Sha’aban yayi kwana 29.
Wannan Shekarar Shehun Borno Alhaji Garbai Umar Elkenemi ke sanarda ganin watan a madadin mai alfarma Sarkin musulmi Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar wanda rahotanni su ka bayyana cewa ba ya kasa.
Wannan shi ne kusan karo na farko a tarihin shekarun nan da Shehun Borno ke ba da sanarwar kuma dama shi ne mataimakin shugaban majalisar sarakuna na Arewa.
Garbai Elkenemi ya bukaci musulmi su yi amfani da damar wajen yi wa shugabanni da kasa addu’ar alheri.
Malamai na kira ga masu hannu da shuni da ma ‘yan kasuwa su sa tallafi ko rangwame a farashin kayan masarufi.
Sheikh Abdullahi Bala Lau babban malami ne na sunnah a Najeriya wanda ya nuna muhimmancin rangwame a watan azumi.
Hakika musulmi kan yi amfani da watan na azumi wajen ninka kwazo a ibada da yin dogayen sallolin nafila.
Tuni majalisun tafsiri sun fara gabatarda zama inda bana Khalifan Shehu Dahiru Bauchi wato Sayyadi Ibrahim Dahiru Bauchi ya bude tafsirin Shehi wanda Allah ya yi wa rasuwa a kwanakin baya. Shehu kan gudanar da tafsirin a Kaduna a tsawon shekaru masu yawa.
Izala kadai ta tura fiye da malamai 2000 a ciki da wajen Najeriya don gabatarda tafsiri.
Ga Cikekken rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya


