Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya
Published: February 18, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Turkiyya Racep Tayyib Erdogan ya ce a ranar Talata, yarda da Isara’ila ta yi da Somaliland a matsayin kasa mai cin gashin kan ta ba zai amfani ita kan ta Somaliland din ko kuma yankin da ta tsage daga ciki ba.

Tun a watan Disambar bara ma shugaban na Turkiyya yayi irin wannan martani inda ya ce shawarar da Isra’ila ta yanke na yarda da Somaliland, wadda ke a yankin arewacin Somalia, da ta yi ikirarin samun ‘yancin kai a matsayin kasa mai cin gashin kan ta a shekarar 1991, ya sabawa doka, ya kuma zargi Isra’ila da son kawo hargitsi a yankin na Afirka.

Turkiyya, wadda ke cikin kungiyar kasashen NATO tana kara tasirin ta a kasashen Afirka a shekarun kwana kwanan nan, inda ta ke horar da jami’an tsaron Somalia, tare da samar da taimakon kawo ci gaban kasa, a madadin bata damar amfani da hanya mai muhimmanci ta fitar da kayyayaki. Yayin da ita kuma kasar Somalia ta Yanke duk wata alaka dake tsakanin ta da kasashen Haddaddiyar Daular Laraba, inda ta zarge su da yin tasiri wajen yarda da Somaliland da Isra’ila ta yi a matsayin kasa mai ‘yancin kai.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan
Next Post: ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi

Karin Labarai Masu Alaka

Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
  • Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
  • Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
  • Hamas Ta Kwance Damara Afrika
  • Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.