Shugaban Amurka Donald Trump, ya fadawa taron farko na kwamitin wanzar da zaman lafiya da ya kafa a ranar Alhamis cewa, kasashe da suke cikin kwamitin sun bada gudumawar kudi dala bilyan bakwai 7, domin sake gine Gaza da zarar Hamas ta kwance damara, burin na ajiya makamai tabbatarsa zai yi wuyan gaske.
Tilas ta Hamas ta ajiye makamanta da janyewar sojojin Isra’ila daga zirin, yawan kudaden da aka tara domin aikin sake gine zirin, da tura kayan agaji ga mazauna yankin da yakin ya daidaita su, sune batutuwa da za su zamo zakaran gwajin dafi na tasirin wannan kwamiti.
A jawabinsa mai tsawo, shugaba Trump ya sanar da wakilan kasashe 47 da suka halarci zaman kwamitin cewa, Amurka zata bada gudumawar kudi dala bilyan 10 ga ayyukan kwamitin wanzar da zaman lafiyan.
Shugaban na Amurka yace kungiyar kwallon kafa ta duniya FIFA zata tara kudi dala milyan 75 domin raya kwallon kafa a Gaza, yayinda MDD zata bada gudunmawar dala bilyan biyu domin ayyukan raya al’uma.


