Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka
Published: February 21, 2026 at 8:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 23, 2026

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ranar Asabar yace hukuncin da kotun kolin Amurka ta yanke ranar jumma’a akan harajin da shugaba Trump yake azawa cinikayya da Amurka, yace yana da kyau hakan, ya kasance akwai sashen gwamnati da zai iya takawa wani sashe birki, karkashin tsarin Dimokraɗiyya.

“Babu laifi idan ana da kotun koli, ma’ana akwai doka da oda,” Macron ya fada da yake amsa tambaya dangane da hukuncin da kotun kolin Amurkan ta yanke ranar jumma’a cewa matakan harajin da shugaba Trump ya dauka a baya, basa bisa doka.

Ya kara da cewa Faransa zata yi nazarin makomar sabon harajin na kashi 10 cikin dari ga dukkan kasashen duniya masu hulda da Amurka ta fuskar kasuwanci, domin inji Macron, Faransa tana son ta ci gaba da sayar da kayayyaki da take sarrafawa da suka hada da kayan amfanin gona, kayan alatu, da kwanbo, da kuma ta fuskar jiragen sama.

Yace akwai bukatar ya kasance akwai tsinkaya, inda kasashe za su sakawa juna, ba wai kawai a yi ta gaban kai wajen mu’amala da ba.

Ahalinda ake ciki kuma, dubban ‘yan Faransa ne suka yi maci a yau Asabar a birnin Lyon, inda a makon jiya aka kashe wani mai ra’ayin mazan jiya, da ake zargin ‘yan tsantsi ne suka masa duka har lahira. Lamari da yayi matukar kada ‘yan kasar.

‘Yan sanda sun bayyana damuwar macin na yau Asabar ya zama tarzoma saboda birnin na Lyon yana cike da masu ra’ayin rikau da kuma ‘yan tsantsin.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu
Next Post: Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya

Karin Labarai Masu Alaka

Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Sarakunan Gumel Da Zurmi Labarai
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Gombe Ta Yi Kira Ga Jami’o’i Su Tallafa Wa Gwamnati Ta Hanyar Bincike Da Ƙirƙire-ƙirƙire Afrika
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.