Babban Bankin Najeriya ya rage kudin ruwa da rabin maki ko rabin kashi daya cikin dari a ranar talatan nan, yana mai cewa a hasashen sa ya auna dai dai game da kasadaf dake tattare da tattalin arziki, kuma yana ganin farashin kayayyaki zai kara faduwa.
Wannan shawara na babban bankin ya tsaida kudin ruwa kan kashi 26 da rabi, ya haura da kadan kan ra’ayoyin masana tattalin arziki, wadanda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya nemi jin ra’ayoyinsu gabannin babban bankin na Najeriya ya tsaida shawara.
Gwamnan babban bankin Olayemi Cardoso ya gayawa taron manema labarai cewa matakan tsuke bakin aljihu da aka dauka a baya, samun daidaito ta fuskar canjin kudi, da kuma wadatar abinci suna daga cikin dalilai da suke rage hauhawara farashin kayayyaki.
A senegal kuma, ministan kudin kasar Chiekh Diba, ya fadawa wakilan majalisar dokokin kasar ranar talata cewa, har yanzu akwai gibi ko banbancin ra’ayi mai yawa tsakanin kasar da asusun bada lamuni na duniya wato IMF a takaice, a kokarin da kasar take yi na neman bashi daga hanun asusun.


