Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa
Published: February 26, 2026 at 4:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Akalla mutane 25 ne aka kashe tare da kona gidaje da dama bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wasu kauyuka biyu, da yammacin ranar Talata a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya, kamar yadda mazauna yankin da gwamnan jihar suka bayyana a ranar Laraba.

Maharan sun kai hari a Kirchinga da ke gundumar Madagali da Garaha da ke makwabtaka da Hong, kauyuka biyu da ke gefen dajin Sambisa inda mayakan Boko Haram da kungiyar IS da ke yammacin Afirka ke kai hare-hare.

Tawayen hare-haren dai na nuna rashin tsaro da ake fama da shi a yankin arewa maso gabashin Najeriya, inda aka shafe shekaru 17 ana tada kayar baya, duk kuwa da yakin da sojoji suka yi na tsawon shekaru.

Abubakar Lawan Kanuri, hakimin kauyen Kirchinga, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa maharan sun isa kauyen ne da yammacin ranar Talata sanye da kakin soji wanda da farko ya sa mazauna garin suka yi kuskuren cewa sojoji ne da ke sintiri. Ya ce an gano gawarwakin mutane 18 bayan da ‘yan bindigar suka ratsa cikin al’umma.

A Garaha, mutane bakwai ne suka mutu a lokacin da wasu ‘yan bindiga a kan babura sama da 50 suka far wa kauyen inda suka kai hari a wani sansanin soji da ke kusa da wurin, in ji wani mazaunin garin Musa Isa, ya kuma kara da cewa “da kyar ya tsere”.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka
Next Post: Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar

Karin Labarai Masu Alaka

Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu Wasanni
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
  • Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.