Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa
Published: February 26, 2026 at 4:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Akalla mutane 25 ne aka kashe tare da kona gidaje da dama bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wasu kauyuka biyu, da yammacin ranar Talata a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya, kamar yadda mazauna yankin da gwamnan jihar suka bayyana a ranar Laraba.

Maharan sun kai hari a Kirchinga da ke gundumar Madagali da Garaha da ke makwabtaka da Hong, kauyuka biyu da ke gefen dajin Sambisa inda mayakan Boko Haram da kungiyar IS da ke yammacin Afirka ke kai hare-hare.

Tawayen hare-haren dai na nuna rashin tsaro da ake fama da shi a yankin arewa maso gabashin Najeriya, inda aka shafe shekaru 17 ana tada kayar baya, duk kuwa da yakin da sojoji suka yi na tsawon shekaru.

Abubakar Lawan Kanuri, hakimin kauyen Kirchinga, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa maharan sun isa kauyen ne da yammacin ranar Talata sanye da kakin soji wanda da farko ya sa mazauna garin suka yi kuskuren cewa sojoji ne da ke sintiri. Ya ce an gano gawarwakin mutane 18 bayan da ‘yan bindigar suka ratsa cikin al’umma.

A Garaha, mutane bakwai ne suka mutu a lokacin da wasu ‘yan bindiga a kan babura sama da 50 suka far wa kauyen inda suka kai hari a wani sansanin soji da ke kusa da wurin, in ji wani mazaunin garin Musa Isa, ya kuma kara da cewa “da kyar ya tsere”.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka
Next Post: Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sakamakon Yakin Gabas Ta Tsakiya Kowacce Gangar Mai Ta Haura Dala 100 Afrika
  • Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027 Siyasa
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.