Adadin mutanen da suka rasa rayukan su a harin da wasu mutane da ba’a san ko su waye ba suka kai yankin gudanarwa na Ruweng a Sudan ta kudu ya kai 169, inda aka samu kari kan kiyasin baya na mutane 122 da aka yi a cewar ministan sadarwa na kasar a ranar Litinin.
Tashin hankali a kasar yayi tsamari a watannin baya bayan nan, abinda ke barazanar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka wanza a shekarar 2018.
Harin na kwanan nan ya auku ne a Abiemnhom a Ruweng, lokacin da matasa daga yankin Mayom a jihar Unity suka farma garin, aka rinka gwabza fada fiye da tsawon sa’o’i 3, a cewar ministan sadarwa James Monyluak. Daga cikin wadanda aka kashe 90 fararen hula ne, 79 kuma sojojin gwamnati. Adadin mamatan zai iya karuwa inji ministan.


