Prime ministan kasar Senegal Ousmane Sonko ya ce a shirye yake da ya sauya shekar jam’iyya ta gwamnati ya koma jam’iyyar adawa idan shugab Bassirou Diomaye Faye ya karkata daga manufar jam’iyyar.
Ana zaman zullumi a kasar bayan da aka samu tashin hankali a jami’o’i, da kuma doguwar magana tare da asusun bada lamuni na duniya wato IMF, yayin da Senegal ke kokarin hada kudade, ta kuma tattauna sabon tsari na samun rance daga asusun na IMF. Sabani tsakanin shugabannin biyu zai iya kawo tsaiko wajen tattaunawa da IMF din.
IMF ta tsaida shirin bada tallafi na dala miliyan dubu 1 da dubu dari takwas a shekarar 2024 bayan da gwamnatin Sonko ta bankado Wasu basussuka da gwamnatin baya ta gaza bayyana su da suka kai kiyasin dala miliyan dubu 11.


