Ayayin da hankalin duniya ya karkata akan yakin da ya barke tsakanin Amurka da isra’ila da Kuma Kasar Jamhuriyar Musulunci ta Iran masana harkokin diplomasiyya na ci gaba da sharhi akan makomar kasashe irin na Africa akan wannan yaki,
Tun bayan kisan jagoran Addini na Kasar ta Iran dama wasu manyan Jami,an Gwamnatin Kasar ciki harda tsohon Shugaban Kasar Ahmadi Najad aka shiga fargaba akan yadda zata kasance da Kuma yadda yakin zai shafi Sauran kasashen duniya,
Tsohon jakadan Najeriya a Kasar Afrika ta Kudu Ambasada Ahmed Musa Ibeto yace ko shakka babu Wannan yaki zai shafi kasashen Afrika Musamman Najeriya ta fuskar tattalin Arziki saboda haka akwai bukatar karatun ta natsu.
Dr. Abubakar kawu Hassan Malami ne a kwalejin ilimi ta Ummaru sanda Ahmadu dake Birnin Minna yace lamarin ba karamin bala’i bane domin kuwa ya shafi Addini kai tsaye.
A yanzu dai lokaci ne yayi da sauran kasahen larabawa dake gabas ta tsakiya suyima kansu karatun ta natsu akan abinda yake faruwa da kasar ta irin da abaya kasar Amurka tayi Amfani da ita wajan tarwatsa kasar Iraqi wannan shine ra’ayin Dr. Ishaka Ibrahim na kwalejin ilimi ta jihar Neja.
Ayanzu dai masanan siyasar duniya na Ganin Koba komi Shugaban Amurka ya Fara cimma maradunsa na biyawa yahudawa Bukata kamar yadda ya dauko alkawari tunda farko kamar yadda Ambasada Ahmed Musa Ibeto ya bayyana.
Ayanzu dai kallo ya Koma gabas ta tsakiya ayayin da ake ci gaba da luguden wuta tsakanin kasar ta Iran da Isra’ela da kuma uwargijiyar Kasar yahudun Wato Amurka.


