Awani taron manema labarai a Minna Kwamishinan Ma’aikatar Kasa da safiyo na Jihar Barista Bello Muhammad Agwara yace wadanda aka soke lasisin nasu sun kasa cika ka’idojin da Gwamnatin Jihar ta basu na bunkasa filayen cikan wa,adin da aka dibar masu,
Wadan nan filaye guda 20 dai Akwai kimanin yawan hekta ko kadada kimanin 40,000 a cikinsu wasu daga cikinsu Manyan gonaki ne na wasu kamfanoni a Najeriyar.
Barista Bello Agwara yace Gwamnati na Bukatar masu Bunkasa Jihar ne ta hanyar Samar da kamfanoni da filayen da Gwamnati ta Basu.
Samun takardar Mallakar fili daga Gwamnati abu ne mai matukar Daukar lokaci a tsarin Hukumomin Najeriya Amma a yanzu Gwamnatin Jihar Neja tace ta bude kofa ga duk Wani Mai Bukatar lasisin cikin karamin lokaci a Jihar Neja kamar yadda Kwamishinan yayi Karin bayani.
Jihar Nejan Mai iyaka da Abuja Fadar Gwamnatin Najeriya na shirin samar da filayen domin samar da Masana,antu a Manyan birane na Jihar a ciki harda Yankin suleja Lamarin da Masana tattalin Arziki sukace zai taimaka wajan janyo Hankalin masu zuba jari daga sassan duniya.
Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana a Jihar Nejan Najeriya Mustapha Nasiru Batsari Yana dauke da cikekken rahoton


