Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu
Published: November 24, 2025 at 11:29 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 25, 2025

Gwamnan Jihar Gombe, ya bayar da umarnin rufe dukkan makarantun jihar daga yanzu zuwa ranar Juma’a, 28 ga Nuwamba, 2025.

Shugaban Hukumar ilimi matakin farko a Jihar Gombe, wato SUBEB, Farfesa Esrom Jocthan Toro, ne ya isar da umarnin gwamnan yayin taro da ya gudanar da dukkan Sakatarorin Ilimi na ƙananan hukumomi a ofishinsa.

Farfesa Esrom ya tabbatar da kudirin Gwamna Inuwa Yahaya na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a, yana mai cewa umarnin rufe makarantu mataki ne na kariya domin kauce wa duk wani lamari marar dadi.

Ya ce dukkan jarabawa za a gudanar da su tsakanin yau da ranar Juma’a 28, tare da kira ga iyaye da kada su shiga damuwa domin gwamnati na ƙoƙarin tabbatar da tsaro yadda ya kamata.

Shugaban SUBEB ɗin ya kuma umarci dukkan Sakatarorin Ilimi da su tanadi duk bayanan da suka shafi makarantun da ke karkashin su, domin kwamitin farfaɗo da makarantun zai fara zagayawa wasu daga cikin makarantun da aka zaɓa domin tantancewa da nazari, kafin a bayar da shawarwari.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC
Next Post: Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai
Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
  • Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.