Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC
Published: March 12, 2026 at 7:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanata Aminu Waziri Tambuwal, tsohon Gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Mazabar Sokoto ta Kudu, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

A cikin wata wasika mai kwanan wata 11 ga Maris, 2026 wadda ya aikewa da shugaban jam’iyyar PDP na gundumarsa ta Tambuwal/Shinfiri da ke Karamar Hukumar Tambuwal a jihar Sokoto, Sanata Tambuwal ya bayyana cewa ya ajiye zama dan jam’iyyar PDP nan take.

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai a Najeriyan ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne bayan zurfin tunani da kuma tuntuba mai fadi da abokan siyasa da magoya bayansa.

A cewarsa, rikice-rikicen cikin gida, sabanin ra’ayi tsakanin shugabannin jam’iyyar da kuma rarrabuwar kawuna da ke ci gaba da addabar PDP sun sa ya zama da wahala a gare shi ya ci gaba da kasancewa a cikinta.

Ya kara da cewa wadannan matsaloli sun raunana hadin kai da kuma alkiblar da jam’iyyar ta tsaya a kai a baya.

Sanata Tambuwal ya kuma nuna godiyarsa ga jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi ya yi wa kasa hidima a mukamai daban-daban, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai da kuma Gwamnan jihar Sokoto na wa’adi biyu.

Bayan sanar da ficewarsa daga PDP, Sanata Tambuwal ya tabbatar da cewa ya shiga jam’iyyar ADC tare da wasu daga cikin abokan siyasa da magoya bayansa.

Ya bayyana cewa matakin ya samo asali ne daga yakinin da yake da shi na cewa Najeriya na bukatar wata dandalin siyasa mai karfi da za ta ginu kan gaskiya, rikon amana, hada kai da kuma cikakken kudurin bunkasa kasa.

Sanatan ya sake jaddada aniyarsa ta ci gaba da yi wa Najeriya hidima tare da kare muradun dimokuradiyya, adalci da hadin kan kasa.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF
Next Post: Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika
Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno Afrika
Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.