Kasar Ghana tayi niyyar gabatar da shawara ga Majalisar Dinkin Duniya na kudurin amincewa da fataucin bayi zuwa kasashen yamma a matsayin laifi mafi muni a tarihin dan Adam, da kuma kira da a biya diyya. Ghana na sa ran samun goyon baya sosai duk da turjiya daga Turai.
Kasar ta yammacin Afirka na shirin gabatar da kudurin nata ga babban Taron Majalisar Dinkin Duniya mai yiwuwa a farkon wannan watan, a cewar ma’aikatar harkokin wajen kasar a wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Wannan shirin wani mataki ne na kokarin da Afirka ke yi na bin ba’asi kan rashin adalcin da turawan mulkin mallaka suka tafka a baya, kuma Ghana na sa ran samun goyon baya daga kasashe da dama.


