Shugaban Amurka Donald Trump yayi watsi da kokarin da ‘yan kawancen Amurka na kasashen yankin Gabas ta Tsakiya suke yi na a fara tattaunawar diplomasiyya don kawo karshen yaki da Iran, wanda aka fara mako biyu da suka wuce, a cewar wasu majiyoyi biyu dake da masaniya kan abun.
A nata bangaren, kasar Iran ta ki yarda da duk wani yunkuri na tsagaita wuta, har sai hare-haren da Amurka da Isra’ila ke kaiwa sun tsaya, kamar yadda wasu manyan jami’an Iran su biyu suka shaidawa kamfanin Dillancin Labarai na Reuters, inda suka kara da cewa kasashe da dama suna kokarin sulhuntawa don kawo karshen yakin.
Wannan turjiya da rashin amincewa tsakanin kasashen biyu, na nuni da cewa yakin zai iya daukan tsawon lokaci ana yi, duk da barnar rayuka da ake tayi, ga kuma hauhawar farashin man fetur sakamakon rufe mashigan ruwa na Hormuz da Iran ta yi


