Zarge-zargen aikata ba daidai ba na lalata da aka yi wa babban mai gabatar da ƙara na Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) na ci gaba da kasancewa ƙarƙashin nazari daga ɓangaren zartarwa na kotun, a cewar wata takardar cikin gida da aka rabawa ma’aikata jiya Lahadi, wadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.
Babban mai gabatar da ƙara na ICC, Karim Khan, wanda ke binciken laifukan yaƙi, laifukan cin zarafin bil’adama da kuma kisan kare dangi, ya janye daga aikinsa na ɗan lokaci domin ba da dama ga bincike kan zargin cewa yana da wata alaƙar ta cin zarafin wata lauya a ofishinsa ba tare da amincewarta ba. Ya musanta aikata wani laifi.
Lauyoyin Khan sun bayyana a martanin su da suka bayar bayan Reuters ta wallafa rahotonta ranar Lahadi cewa ana sa ran hukumar tafiyar da ICC za ta gana a yau Litinin domin duba shawarwari da sakamakon da wani kwamiti na alkalai masu zaman kansu ya bayar, wanda har yanzu ba a bayyana shi ga jama’a ba.
“Alkalan sun gabatar da cikakken nazari mai zurfi tare da hujjoji, inda suka cimma matsaya gaba ɗaya cewa bayanan gaskiya da aka tattara ba su tabbatar da aikata ba daidai ba ko karya doka ba. Abin da ya rage yanzu shi ne shugabannin siyasa a cikin Hukumar gudanarwa su tabbatar da wannan kimantawa da Kwamitin ya yi,” in ji lauyoyin Khan a cikin wata sanarwar imel.


