Ranar talata a New York, shugaban kasar Ghana, John Daramani Mahama, ya soki manufofin gwamnatin Amurka, kan abunda ya kira amincewa da goge tarihin bakar fata, yana mai cewa hakan zai iya shafar wasu lamura sosai.
Tun bayan da ya dawo kan madafun iko, shugaba Donald Trump, ya auna hukumomi da cibiyoyin al’adun gargajiya, da suka hada da wuraren adana tarihi da wasu kayan al’adu, domin cire abunda ya kira “manufofin nuna kiyayya ga Amurka.”
Kalaman shugaba Trump da wasu dokokin shugaban kasa, da ake kira Executive orders, sun kai ga cire wasu kayan tarihin bautar da bakar fata, sake dawo da kayan tarihin turawa masu da’awar wariya, da wasu matakai da masu yakin tabbatar da ‘yancin tsiraru suke ganin zai maida hanun agogo baya.
Wadan nan matakai sun zama manhaja ga wasu gwamnatoci da kungiyoyi ko kamfanoni masu zaman kansu,” inji shugaba John Daramani, lokacin da yake magana a wani lamari a MDD, yace ko babu komi sannu a hankali matakan suna halatta goge tarihi.
Shugaba Mahama yace a Amurka ana cire kososhi da suke koyar da tarihin bakar fata a makarantu, ana tilastawa cibiyoyi su daina koyarda “gaskiyar tarhin bauta da wariyar launin fata,” kuma littatafai da suke karantar da wannan batu ana ci gaba da haramta su.
Shugaba Mahama a bara, ya amince da wani shirin karbar ‘yan asalin Afirka ta yamma da gwamnatin Trump ta tusa keyar su, a baya ya soki shugaba Trump kan karyar da yayi cewa ana yiwa turawa kisan kare dangi tare da kwache musu filaye a Afirka ta kudu, da cewa fadin hakan cin fuska ne ga daukacin Afirka.
Fadar White House bata maida martani nan take kan maganar shugaba John Daramani Mahama.


