Shugaban Amurka Donlad Trump ya ce ‘yan kasar Iran, mutane ne da suka kware wajen tattaunawa kan cimma yarjejeniya, amma ya kara da cewa baya zaton zai yi wata yarjejeniya da su don kawo karshen yakin da Isra’ila da Amurka suke yi da Iran din.
Da yake magana yayin wata tattaunawa da majalisar ministoci a fadar White house, Trum yace yanzu Iran na da damar soke duk wani kudiri nasu na makamashin nukiliya har abada, su sauya manufa. Ya kara da cewa zamu ga idan suna so suyi hakan, idan kuma sun ki, zamu zame musu karfen kafa, mu ci gaba da aika musu da bama bamai.
Jawabin na Trump yayi biyo bayan matsin rayuwa da sanadin yakin ya jawo ke kara tsamari, inda ake fuskantar rashin isasshen man fetur da gas, abinda ya sa kamfanoni da kasashe tashi tsaye wajen kokarin shawo kan lamarin.
Jakadan Amurka na musamman, Steve Witkoff ya tabbatar da cewa Amurka ta aike da takarda mai dauke da ka’idoji 15, a matsayin hanyar da za’a bi don tattaunawa kan kawo karshen yakin, ya kara da cewa akwai alama cewa fadar gwamnatin Tehran nada sha’awar cimma yarjejeniya.
Ministan harkokin waje na kasar Pakistan yace tattaunawa tsakanin Amurka da iran na wanzuwa ne ta hanyar sakonni da ake aikowa ta hannun fadar gwamnatin Islamabad, tare da wasu kasashe da suka hada da Turkiyya da Masar, wanda suma suke goyon bayan tattaunawar sulhu.


