Ranar talata, majalisun dokokin Najeriya suka amince da kari akan Kasafin kudin kasar zuwa Naira trillion 68 da milyan milya dari uku, wato dala bilyan 49 da milyan dubu 400, bayan da shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya bukaci wakilan su amince da canjin domin karfafa shirin da aka gabatar musu tun da farko cikin watan Disamba.
Shugaba Tinubu wanda yake cikin shekara ta uku da hawa kan karagar mulki, ya bullo da shirye shirye na yin garambawul ga tattalin arzikin kasar, da suka hada da janye tallafin mai dana makamashi masu tsada, da karya darajar kudin kasar, hade garambawul ga hanyoyin tara kudin haraji da zummar karfafa Kudaden shiga ga gwamnati.
A ranar 19 ga watan disemba ne shugaba Tinubu ya gabatarwa majalisa kasafin kudi na Naira trillion 58. 47, yana mai cewa zummar itace kara karfafa ci gaban tattalin arziki.
Ahalinda ake ciki kuma, wasu majiyoyi sun fadawa kamfanin dillanciin labarai na Reuters cewa, kamfanin mai na Najeriya NNPC ya kara mai da yake baiwa matatar mai ta Dangote zuwa jirage bakwai daga 5 da ya saba baiwa kamfanin cikin watannnin baya, sakamakon tashin farashin mai da yakin gabas ta tsakiya ya haddasa.


