Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka
Published: April 4, 2026 at 8:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar ‘yan sanda a jihar Filato ta ja kunnen al’ummar yankin Jos ta Arewa kan su tabbatar sun shige gidajen su kafin karfe uku na yamma.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Filato, Alfred Alabo yace jami’an tsaro zasu aiwatar da umurnin da gwamnatin jihar ta bayar na hana fita daga karfe uku na yamma zuwa karfe bakwai na safe, bayan share kwanaki biyu da al’ummar yankin suka yi a kulle.

Jami’in ‘yan sandan yace duk wanda aka kama a titi kan kowani dalili, hukuma zata kama shi ya fuskanci hukunci.

Alfred Alabo ya kuma ce sun tattauna da shugaban jami’ar Jos, Farfesa Tanko Ishaya don neman hanyoyin kai dalibai dake bukatar komawa gidajensu zuwa garuruwansu.

Kakakin ‘yan sandan na jihar Filato yace basa son hankalin daliban ya tashi, shi ya sa kwamishinan ‘yan sanda a jihar ya bada umurnin a samarda tsaro a gidajen kwanan daliban da ma harabar jami’ar baki daya.

Rikicin a ranar Laraba ya sake barkewa a cikin garin Jos, bayan gwamnatin jihar ta sassauta dokar hana fita na kwanaki biyu da ta sanya a karamar hukumar Jos ta Arewa.

Duk da shike lamarin ya lafa, bayanai na nuni da cewa rayuka sun hallaka, wassu sun sami raunuka, yayinda ‘yan kasuwa suka rurrufe hajjarsu suka gudu.

Sheikh Farouk Omar, na’ibin limamin masallacin Haibar dake Jos, yace sai gwamnati ta jajirce wajen tabbatar da hukunci kan wadanda ta samu da laifi, shine zai samadda zaman lafiya.

Shima Pharmacist Markus Kanda yace kamata yayi hukumomi su dauki matakan tsaro da zarar ga alamun tashin hankali.

A ranar Alhamis ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Tinubu zai kawo ziyarar jaje wa al’ummar jihar Filato, biyo bayan harin da wassu ‘yan bindiga suka kai kan al’ummar jihar a Angwan Rukuba, da ma yamutsin da ya auku a jiya Laraba da yayi sanadin rasa wassu rayuka a wassu sassan garin na Jos.

Daga Jos Ga Rahoton Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260404-WA0006.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia
Next Post: Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
‘Yan Sandan Gombe Sun Yi Taron Gaggawa Da Jam’iyyun Siyasa Da INEC Kan Tsaro Labarai
Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.