Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka
Published: April 4, 2026 at 8:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar ‘yan sanda a jihar Filato ta ja kunnen al’ummar yankin Jos ta Arewa kan su tabbatar sun shige gidajen su kafin karfe uku na yamma.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Filato, Alfred Alabo yace jami’an tsaro zasu aiwatar da umurnin da gwamnatin jihar ta bayar na hana fita daga karfe uku na yamma zuwa karfe bakwai na safe, bayan share kwanaki biyu da al’ummar yankin suka yi a kulle.

Jami’in ‘yan sandan yace duk wanda aka kama a titi kan kowani dalili, hukuma zata kama shi ya fuskanci hukunci.

Alfred Alabo ya kuma ce sun tattauna da shugaban jami’ar Jos, Farfesa Tanko Ishaya don neman hanyoyin kai dalibai dake bukatar komawa gidajensu zuwa garuruwansu.

Kakakin ‘yan sandan na jihar Filato yace basa son hankalin daliban ya tashi, shi ya sa kwamishinan ‘yan sanda a jihar ya bada umurnin a samarda tsaro a gidajen kwanan daliban da ma harabar jami’ar baki daya.

Rikicin a ranar Laraba ya sake barkewa a cikin garin Jos, bayan gwamnatin jihar ta sassauta dokar hana fita na kwanaki biyu da ta sanya a karamar hukumar Jos ta Arewa.

Duk da shike lamarin ya lafa, bayanai na nuni da cewa rayuka sun hallaka, wassu sun sami raunuka, yayinda ‘yan kasuwa suka rurrufe hajjarsu suka gudu.

Sheikh Farouk Omar, na’ibin limamin masallacin Haibar dake Jos, yace sai gwamnati ta jajirce wajen tabbatar da hukunci kan wadanda ta samu da laifi, shine zai samadda zaman lafiya.

Shima Pharmacist Markus Kanda yace kamata yayi hukumomi su dauki matakan tsaro da zarar ga alamun tashin hankali.

A ranar Alhamis ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Tinubu zai kawo ziyarar jaje wa al’ummar jihar Filato, biyo bayan harin da wassu ‘yan bindiga suka kai kan al’ummar jihar a Angwan Rukuba, da ma yamutsin da ya auku a jiya Laraba da yayi sanadin rasa wassu rayuka a wassu sassan garin na Jos.

Daga Jos Ga Rahoton Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260404-WA0006.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia
Next Post: Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a Sauran Duniya
Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya
  • Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump
  • Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara
  • An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.