Hukumar ‘yan sanda a jihar Filato ta ja kunnen al’ummar yankin Jos ta Arewa kan su tabbatar sun shige gidajen su kafin karfe uku na yamma.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Filato, Alfred Alabo yace jami’an tsaro zasu aiwatar da umurnin da gwamnatin jihar ta bayar na hana fita daga karfe uku na yamma zuwa karfe bakwai na safe, bayan share kwanaki biyu da al’ummar yankin suka yi a kulle.
Jami’in ‘yan sandan yace duk wanda aka kama a titi kan kowani dalili, hukuma zata kama shi ya fuskanci hukunci.
Alfred Alabo ya kuma ce sun tattauna da shugaban jami’ar Jos, Farfesa Tanko Ishaya don neman hanyoyin kai dalibai dake bukatar komawa gidajensu zuwa garuruwansu.
Kakakin ‘yan sandan na jihar Filato yace basa son hankalin daliban ya tashi, shi ya sa kwamishinan ‘yan sanda a jihar ya bada umurnin a samarda tsaro a gidajen kwanan daliban da ma harabar jami’ar baki daya.
Rikicin a ranar Laraba ya sake barkewa a cikin garin Jos, bayan gwamnatin jihar ta sassauta dokar hana fita na kwanaki biyu da ta sanya a karamar hukumar Jos ta Arewa.
Duk da shike lamarin ya lafa, bayanai na nuni da cewa rayuka sun hallaka, wassu sun sami raunuka, yayinda ‘yan kasuwa suka rurrufe hajjarsu suka gudu.
Sheikh Farouk Omar, na’ibin limamin masallacin Haibar dake Jos, yace sai gwamnati ta jajirce wajen tabbatar da hukunci kan wadanda ta samu da laifi, shine zai samadda zaman lafiya.
Shima Pharmacist Markus Kanda yace kamata yayi hukumomi su dauki matakan tsaro da zarar ga alamun tashin hankali.
A ranar Alhamis ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Tinubu zai kawo ziyarar jaje wa al’ummar jihar Filato, biyo bayan harin da wassu ‘yan bindiga suka kai kan al’ummar jihar a Angwan Rukuba, da ma yamutsin da ya auku a jiya Laraba da yayi sanadin rasa wassu rayuka a wassu sassan garin na Jos.
Daga Jos Ga Rahoton Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji


