Shugaban wani bangaren Libya dake gabashin kasar, Khalifa Haftar, ya sayi jiragen yaki da basu da matuka wadanda alamu suka nuna kiran kasar China ne da kuma Turkiyya, kamar yadda wani bincike da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gano, duk da kudurin MDD wadda ya haramta sayar da makamai ga kasar mai gwamnati biyu a arewacin Afirka.
Hotuna da aka dauka da tauraruwar dan ‘Adam, sun nuna akalla jiragen drones uku a tashar jirage na soja dake Bengazi, mai tazarar mel 62 daga Begazin, da aka dauka daga watan Disemba zuwa yanzu. Wadanda babu bayanin saye ko kai su can.
An gani a fili wata na’ura shigen wacce ake yi wa irin wadan nan jiragen jagora da su zaune a fili.
Jiragen yaki marasa matuka sun taka muhimmiyar rawa a yakin da dakarun Haftar suka yi tsakanin shekara ta 2014-20, lokacin da mayakansa suka yi kokarin kifar da gwamnatin kasar da take a Tripoli mai samun goyon bayan DD, kan zargin wai tana bada mafaka ga ‘yan ta’adda da ‘yan banga zargin hukumomi da suke Tripoli suka musanta.


