Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika

Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari
Published: April 11, 2026 at 11:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar  juma’a Iran tace tilas a sakamarta kadarorinta, kuma a tsagaita wuta a Lebanon, kamun ta fara shawarwari da Washington, mataki da ya jefa zaman sulhu da za’a fara yau Asabar, cikin rashin tabbas.

Kakakin majalisar dokokin kasar Mohammed Baqeer Qaibaf ya fada a shafinsa a dandalin X cewa, wadannan bukatu biyu dama an amince da su a magana da suka yi da Washington, saboda haka ba za’a fara shawarwari ba har sai an cikata alkawuran, yayinda ake ci gaba da takaddama kan ainihin sharuddan tsagaita wuta.

Shi ma ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi, ya jaddada haka, ya bukaci da a kawo karshen farmakin da Isra’ila take kaiwa a Lebanon. Ana sa ran duka jami’an biyu na Iran za su kasance a wajen zaman shawarwari da za’a yi, kamar yadda wasu majiyoyi biyu a Pakistan suka fada.

Kodashike babu wani martani nan take daga fadar White house, shugaban Amurka Donald Trump ya fada a wani sako da ya wallafa a shafinsa dandalin sada zumunta da ake kira Truth Social, dalili daya da ya sa har yanzu Farisawan suke da rai shine domin a kulla yarjejeniya da su.

Shugaba Trump wanda bai maida martani kai tsaye kan bukatun da Iran ta gabatar ba, ya gayawa wata jaridar Amurka da ake kira New York Post, cewa, jiragen ruwan yaki ana sake musu shiri da albarusai masu kwari domin su ci gaba da kai farmaki kan Iran, muddin shawarwarin sulhu da za’a yi Iran a Pakistan ya ci tura.

Mataimaki shugaban Amurka JD Vance wanda zai jagoranci tawagar Amurka zuwa taron, yace yana fatan za’a sami kyakyawar sakamakon taron da za su yi, ya kara da cewa, “Idan kuma za su kokarin su yaudare mu, za su fuskanci turjiya daga tawagar.”

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur
Next Post: Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa

Karin Labarai Masu Alaka

Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • An Kaddamar Da Rigakafin Cutar HIV AIDS A Kasar Zimbabwe Kimiya
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.