Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari
Published: April 11, 2026 at 11:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar  juma’a Iran tace tilas a sakamarta kadarorinta, kuma a tsagaita wuta a Lebanon, kamun ta fara shawarwari da Washington, mataki da ya jefa zaman sulhu da za’a fara yau Asabar, cikin rashin tabbas.

Kakakin majalisar dokokin kasar Mohammed Baqeer Qaibaf ya fada a shafinsa a dandalin X cewa, wadannan bukatu biyu dama an amince da su a magana da suka yi da Washington, saboda haka ba za’a fara shawarwari ba har sai an cikata alkawuran, yayinda ake ci gaba da takaddama kan ainihin sharuddan tsagaita wuta.

Shi ma ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi, ya jaddada haka, ya bukaci da a kawo karshen farmakin da Isra’ila take kaiwa a Lebanon. Ana sa ran duka jami’an biyu na Iran za su kasance a wajen zaman shawarwari da za’a yi, kamar yadda wasu majiyoyi biyu a Pakistan suka fada.

Kodashike babu wani martani nan take daga fadar White house, shugaban Amurka Donald Trump ya fada a wani sako da ya wallafa a shafinsa dandalin sada zumunta da ake kira Truth Social, dalili daya da ya sa har yanzu Farisawan suke da rai shine domin a kulla yarjejeniya da su.

Shugaba Trump wanda bai maida martani kai tsaye kan bukatun da Iran ta gabatar ba, ya gayawa wata jaridar Amurka da ake kira New York Post, cewa, jiragen ruwan yaki ana sake musu shiri da albarusai masu kwari domin su ci gaba da kai farmaki kan Iran, muddin shawarwarin sulhu da za’a yi Iran a Pakistan ya ci tura.

Mataimaki shugaban Amurka JD Vance wanda zai jagoranci tawagar Amurka zuwa taron, yace yana fatan za’a sami kyakyawar sakamakon taron da za su yi, ya kara da cewa, “Idan kuma za su kokarin su yaudare mu, za su fuskanci turjiya daga tawagar.”

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur
Next Post: Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa

Karin Labarai Masu Alaka

Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
Kaduna: Masana Sun Nemi A Sauya Tsohon Wurin Zubar Da Shara Na Tudun-Ilu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika
  • Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.