Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu
Published: April 24, 2026 at 3:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana cewa Najeriya ta shiga wani sabon babi na gyara da ci gaba a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ta buƙaci kafofin yaɗa labarai na duniya da su riƙa rahoton gaskiyar abin da ke faruwa a ƙasar.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin wata tattaunawa ta musamman da wakilan gidajen jaridun ƙasashen waje a Abuja.

Ministan ya bayyana cewa a shekarar 2025, tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.87 cikin ɗari, wanda hakan ke nuna cewa ci gaban tattalin arzikin ya fi ƙaruwar yawan jama’a sauri a karon farko cikin kusan shekara goma.

A cewarsa, cire tallafin man fetur da gyara tsarin musayar kuɗi sun taimaka kwarai wajen tara kuɗaɗen da ake amfani da su yanzu wajen samar da manyan ayyuka da inganta rayuwar al’umma.

Alhaji Mohammed Idris ya jero wasu daga cikin muhimman nasarorin da aka samu, waɗanda suka haɗa da:
• Samar da lamunin karatu ga ɗalibai ta hanyar asusun NELFUND.
• Inganta harkar tsaro ta hanyar amfani da bayanan sirri da leken asiri.
• Yunkurin kafa ’yan sandan jihohi domin bai wa hukumomin gida yancin cin gashin kansu.
• Zuba jari a fannin noma da fasahar zamani domin samar wa matasa ayyukan yi.

A nasa jawabin, Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Mista Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa Nijeriya ta fita daga yanayin fargaba, yanzu tana matakin tabbatar da cewa al’umma sun fara jin daɗin waɗannan gyare-gyare a cikin rayuwarsu ta yau da kullum.

Haka ita ma Ministar Masana’antu da Kasuwanci, Dr. Jumoke Oduwole, ta jaddada cewa Nijeriya ba kawai tana binsu a bayan Afirka ba ne, tana kokarin zama jagora ne a fannin ciniki da masana’antu a faɗin nahiyar.

Minista Idris ya rufe jawabin nasa da kira ga ’yan jaridun duniya da su riƙa bayyana gaskiya game da Nijeriya.

Ya ce: “Muna son a riƙa bayyana nasarorinmu da kuma ƙalubalen da muke fuskanta duka tare, domin hakan ne kawai zai nuna ainihin hoton Nijeriya.”

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Bayo Onanuga da Sunday Dare da kuma Abdulaziz Abdulaziz, waɗanda duka ke tallafa wa shugaban ƙasa a fannin yaɗa labarai da sadarwa.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya.
Next Post: Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya.
  • Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Liverpool Tayi Rashin Nasara A Wasanni Tara Wasanni
  • Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
  • Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.