Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana cewa Najeriya ta shiga wani sabon babi na gyara da ci gaba a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ta buƙaci kafofin yaɗa labarai na duniya da su riƙa rahoton gaskiyar abin da ke faruwa a ƙasar.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin wata tattaunawa ta musamman da wakilan gidajen jaridun ƙasashen waje a Abuja.
Ministan ya bayyana cewa a shekarar 2025, tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.87 cikin ɗari, wanda hakan ke nuna cewa ci gaban tattalin arzikin ya fi ƙaruwar yawan jama’a sauri a karon farko cikin kusan shekara goma.

A cewarsa, cire tallafin man fetur da gyara tsarin musayar kuɗi sun taimaka kwarai wajen tara kuɗaɗen da ake amfani da su yanzu wajen samar da manyan ayyuka da inganta rayuwar al’umma.
Alhaji Mohammed Idris ya jero wasu daga cikin muhimman nasarorin da aka samu, waɗanda suka haɗa da:
• Samar da lamunin karatu ga ɗalibai ta hanyar asusun NELFUND.
• Inganta harkar tsaro ta hanyar amfani da bayanan sirri da leken asiri.
• Yunkurin kafa ’yan sandan jihohi domin bai wa hukumomin gida yancin cin gashin kansu.
• Zuba jari a fannin noma da fasahar zamani domin samar wa matasa ayyukan yi.
A nasa jawabin, Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Mista Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa Nijeriya ta fita daga yanayin fargaba, yanzu tana matakin tabbatar da cewa al’umma sun fara jin daɗin waɗannan gyare-gyare a cikin rayuwarsu ta yau da kullum.
Haka ita ma Ministar Masana’antu da Kasuwanci, Dr. Jumoke Oduwole, ta jaddada cewa Nijeriya ba kawai tana binsu a bayan Afirka ba ne, tana kokarin zama jagora ne a fannin ciniki da masana’antu a faɗin nahiyar.
Minista Idris ya rufe jawabin nasa da kira ga ’yan jaridun duniya da su riƙa bayyana gaskiya game da Nijeriya.
Ya ce: “Muna son a riƙa bayyana nasarorinmu da kuma ƙalubalen da muke fuskanta duka tare, domin hakan ne kawai zai nuna ainihin hoton Nijeriya.”
Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Bayo Onanuga da Sunday Dare da kuma Abdulaziz Abdulaziz, waɗanda duka ke tallafa wa shugaban ƙasa a fannin yaɗa labarai da sadarwa.


